ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Matsayi

Guda daga cikin dattawa a Masana’antar Kannywood, wanda ya shafe fiye da shekara 40 a masana’antar a Nijeriya; Malam Isa Bello Ja (Dattijon Arziki) ya bayyana cewa, ko kadan bai dauki wannan sana’a ta dirama ko wasan kwaikwayo da wasa ba.

Amma hakan, ba zai zama dalilin da zai sa ya yi wani abu da zai zubar masa da mutuncin da ya shafe shekara da shekaru yana nema wa kansa ba. Ya kara da cewa, duk wani abun alheri da mutum zai iya samu a sanadiyar sana’arsa; shi ma ya samu a wannan harka ta wasan kwaikwayo, kama daga zama da manyan mutane masu daraja da mutunci da kuma soyayya da kauna da ya samu daga masoya.

  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC
  • Babu Wata Sana’a Da Take Da Daukaka Da Samu Irin Harkar Fim – Hajara Usman 

Amma duk wannan ba zai sa ya fito a matsayin barawo ko dan daudu ko mashayin giya ko kuma mai neman mata ba, domin kuwa tun kafin ya tara iyali yake wannan harka bai yi wani abin ashsha ba; ballantana yanzu da ya tara iyali da surukai da sauran yan’uwa da abokan arziki.

ADVERTISEMENT

“Tun kafin na shiga harkar fim, na yi aiki a wuraren gwamnati da dama da sauran sana’oi, domin kuwa duk wata sana’a a wajena sana’a ce; don Bahaushe na cewa, babu maraya sai rago, zan iya yin dukkannin wata sana’a don na rufawa kaina asiri, saboda haka, akwai bukatar na tsare mutuncina tare kuma da na sana’ata; wadda nake matukar alfahari da ita”, in ji Ja.

Tun bayan fara wannan sana’a ta dirama da na yi kawo yanzu, zan iya cewa; na yi fina-finai fiye da tunanin mai tunani, daga cikinsu akwai wadanda na fi so fiye da sauran, wadannan kuwa su ne kamar ‘Kowa Ya Bar Gida, Bakan Gizo, Hadarin Kasa da sauran makamantansu, duk wadannan fina-finan ko bayan mutuwata idan aka kalla; babu wanda zai yi tir da ni ko kuma a ce iyalina sun ji kunyar ganina a cikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Daga karshe, Bello Ja ya shawarci matasa masu shigowa masana’antar Kannywood; da su dinga tsarkake niyyarsu suna yin aiki tsakaninsu da Allah, sannan kada su yi wani abun ashsha da zai sa a yi wa masu harkar fim kudin goro wajen kiran su da mutanen banza, inda ya ce duk wanda ya jawo aka zagi ‘yan fim, bai kyauta wa mutanen arzikin da ke cikin masana’antar ba.

Matsayi
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.