ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Lashe Zaben Shugaban Kasa – Gwamnan Kwara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce, Allah ne kadai zai hana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu lashe zaben shugaban kasa da za a gudanar a wata mai kamawa.

Gwamnan ya ce “Na yi amanna Allah ba zai hana wannan nagartaccen mutumin cimma burinsa ba. Asiwaju Tinubu mutum ne na kwarai wanda ya yi tasiri sosai ga rayukan mutane da daman gaske.”

  • Kungiyar Dalibai Za Ta Shiga Zanga-Zanga Kan Kara Kudin Makaranta A Nijeriya
  • Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 

Gwamnan ya kara da cewar “Ina da cikakken kwarin guiwar Tinubu zai lashe zaben shugaban kasa.”

ADVERTISEMENT

Gwamnan yana wannan bayanin ne a Ilorin, babbar birnin jihar, a wajen taron addu’o’i na musamman da Kungiyar Magoya Bayan Tinubu da Shettima a Arewa ta Tsakiya, ta shirya kan neman nasarar dan takarar a zaben 2023.

Da ya ke samun wakilcin mataimakinsa, Kayode Alabi, gwamna AbdulRazaq ya kara da cewa, “Tinubu mutum ne na kwarai. Shi din nagartaccen mutum ne.”

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

“Zan sake nanatawa babu wani abin da zai hana Asiwaju cin zaben shugaban kasa baya ga Allah. Na san irin wadannan mutunen kwarai din, Allah ba ya hana musu dama. Babu wani mutum da ya cika dari bisa dari. Allah ne kawai cikakken da ba ya kuskure.”

“Da zarar ya ci zabe, mu kuma za mu ci zabukan 11 ga watan Maris na gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi.

“Ina rokon masu zabe da su zabi Tinubu, su zabi APC daga kasa har sama.”

Shi ma da ke jawabi, Shugaban kungiyar, Sanata Dayo Adeyeye, ya ce Nijeriya na bukatar agajin Tinubu cikin gaggawa.

Ya ce, tabbas Tinubu zai iya shawo kan matsalolin da suke addabar kasar nan da suka shafi na tsaro da tattalin arziki.

Shi kuma jagoran shirya taron, Hon. Oyetunde Ojo, cewa ya yi, “Shafaffu da mai masu juya masu mulki ba za su samu gurbi a gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed ba.”

Ya kara da cewa Tinubu zai gudanar da gwamnati ne mai cike da hangen nesa da bin komai bisa tsari domin sabunta kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Next Post
2023: APC Ta Yi Sa’a Tinubu Ne Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa – Buhari 

Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.