• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Lashe Zaben Shugaban Kasa – Gwamnan Kwara

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Lashe Zaben Shugaban Kasa – Gwamnan Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce, Allah ne kadai zai hana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu lashe zaben shugaban kasa da za a gudanar a wata mai kamawa.

Gwamnan ya ce “Na yi amanna Allah ba zai hana wannan nagartaccen mutumin cimma burinsa ba. Asiwaju Tinubu mutum ne na kwarai wanda ya yi tasiri sosai ga rayukan mutane da daman gaske.”

  • Kungiyar Dalibai Za Ta Shiga Zanga-Zanga Kan Kara Kudin Makaranta A Nijeriya
  • Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 

Gwamnan ya kara da cewar “Ina da cikakken kwarin guiwar Tinubu zai lashe zaben shugaban kasa.”

Gwamnan yana wannan bayanin ne a Ilorin, babbar birnin jihar, a wajen taron addu’o’i na musamman da Kungiyar Magoya Bayan Tinubu da Shettima a Arewa ta Tsakiya, ta shirya kan neman nasarar dan takarar a zaben 2023.

Da ya ke samun wakilcin mataimakinsa, Kayode Alabi, gwamna AbdulRazaq ya kara da cewa, “Tinubu mutum ne na kwarai. Shi din nagartaccen mutum ne.”

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

“Zan sake nanatawa babu wani abin da zai hana Asiwaju cin zaben shugaban kasa baya ga Allah. Na san irin wadannan mutunen kwarai din, Allah ba ya hana musu dama. Babu wani mutum da ya cika dari bisa dari. Allah ne kawai cikakken da ba ya kuskure.”

“Da zarar ya ci zabe, mu kuma za mu ci zabukan 11 ga watan Maris na gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi.

“Ina rokon masu zabe da su zabi Tinubu, su zabi APC daga kasa har sama.”

Shi ma da ke jawabi, Shugaban kungiyar, Sanata Dayo Adeyeye, ya ce Nijeriya na bukatar agajin Tinubu cikin gaggawa.

Ya ce, tabbas Tinubu zai iya shawo kan matsalolin da suke addabar kasar nan da suka shafi na tsaro da tattalin arziki.

Shi kuma jagoran shirya taron, Hon. Oyetunde Ojo, cewa ya yi, “Shafaffu da mai masu juya masu mulki ba za su samu gurbi a gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed ba.”

Ya kara da cewa Tinubu zai gudanar da gwamnati ne mai cike da hangen nesa da bin komai bisa tsari domin sabunta kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbdulrazaqAPCGwamnan KwaraTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dubun Mutumin Da Ya Shirya Sace Mahaifinsa Ta Cika A Kwara

Next Post

Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Related

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

16 hours ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

1 day ago
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan
Tattaunawa

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

2 days ago
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
Siyasa

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2 days ago
Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano
Siyasa

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

4 days ago
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
Manyan Labarai

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

4 days ago
Next Post
2023: APC Ta Yi Sa’a Tinubu Ne Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa – Buhari 

Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.