• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Dole Ne Karfin Soja Ya Haifar Da Tsaro Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan, juyin mulkin da ya abku a kasar Niger ya girgiza mutanen duniya. Sai dai wani abun da ya fi ba mutane mamaki, shi ne an ce abkuwar lamarin na da alaka da tallafin da kasar Amurka ta ba kasashen yammacin Afirka ta fuskar aikin tsaro.

Wani shafin yanar gizo na kasar Amurka mai suna “The Intercept” ya ba da labarin cewa, birgadiya janar Moussa Barmou, kwamandan rundunar sojojin kundumbala ta kasar Niger, wanda ke da hannu cikin juyin mulkin din da ya abku a kasar a wannan karo, ya taba samun horo a cibiyar horar da sojoji ta Fort Benning ta kasar Amurka da jami’ar koyon ilimin aikin tsaro ta kasar, kuma yana da alakar kut-da-kut da bangaren sojojin kasar Amurka.

  • Ina Dalilin Da Ya Sa Amurka Ta Hura Wutar Rikici Game Da “Yin Takara A Sararin Samaniya” Tare Da Kasar Sin A Argentina?

A cewar shafin yanar gizo na “The Intercept”, a shekarun nan, yawan abkuwar hare-haren ta’addanci a yankin yammacin Afirka ya sa kasar Amurka ta samar da karin tallafin aikin soja da ta ga ya dace ga kasashen dake yankin, sai dai batun nan na haddasa matsaloli: Tun daga shekarar 2008, hafsoshin da suka taba samun horon da bangaren Amurka ya bayar sun shiga juyin mulki guda 11 da suka taba abkuwa a yankin yammacin Afirka. Kana a kasashen Burkina Faso da Mali, dake makwabtaka da kasar Niger, hafsoshin da kasar Amurka ta horar da su sun kaddamar da juyin mulki a kalla sau 6, tun daga shekarar 2012.

A ganin Stephanie Savell, daya daga cikin darektoci masu kula da aikin nazarin kudin da aka kashe da hasarar da aka samu wajen yaki na jami’ar Brown ta kasar Amurka, kana kwararriya mai nazarin matakan aikin soja da kasar Amurka ta dauka a yammacin Afirka, babban dalilin da ya haddasa matsaloli a kasar Niger da yankin Sahel gaba daya bai shafi aikin soja ba, saboda haka yadda gwamnatin kasar Amurka take dora muhimmanci kan samar da makamai ga yankin da horar da sojojin kasashen yankin ba zai taimakawa daidaita matsalar da ake fuskanta ba. A cewarta, “Wani mummunan sakamakon da matakin ya haifar shi ne, raunana karfin shawo kan yanayi na sauran hukumomin gwamnatocin yankin, da karfafa karfin rundunar sojoji a kai a kai. Wannan wani dalili ne da ya sa ake samun dimbin juyin mulki a kasashen Niger, da Burkina Faso, da sauran kasashe daban daban.”

Hakika kasar Amurka ta samar da wannan nau’in tallafin aikin soja ne bisa ra’ayinta kan aikin tsaro. A ganin kasar Amurka, muddin dai akwai cikakken karfin soja, to, za a samu cikakken tsaro. Wannan ra’ayi ya sa kasar ta kashe dimbin kudi wajen raya bangaren soja, har ma yawansa ya kai kashi 39% na kudin da daukacin kasashen duniya suka kashe a shekarar 2022 don raya aikin soja, da sanya kasar kafa cibiyoyin soja kimanin 750 a kasashe da yankuna fiye da 100, da girke sojojinta kimanin dubu 173 a cikin cibiyoyin. Amma ko da yake kasar Amurka ta samu cikakken karfin soja, abun nan bai kawo mata cikakken tsaro ba. Maimakon haka, ya haddasa rushewar manyan gine-gine na World Trade Center a yayin harin da aka kai birnin New York a ranar 11 ga watan Satumban shekarar 2001, da yadda kasar Amurka ta kaddamar da yaki kai tsaye ko kuma a kaikaice, a kasashen Iraki, da Afghanistan, da Libya, da Ukraine, da dai sauransu, inda ta salwantar da rayukan sojojinta, da kudin jama’arta, gami da haifar ma sauran kasashe da babban rashi da dimbin wahalhalu.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Ganin haka ya sa kasar Sin ta gabatar da shawarar kare tsaro a duk duniya, inda ta yi kira da a daidaita rikici ta hanyar yin musayar ra’ayi da shawarwari cikin lumana. Kana kasar ta yi kira da a dukufa a fannin raya tattalin arziki, don daidaita matsalar samun rikici da rashin tsaro daga tushe, da tabbatar da samun yanayin tsaro mai dorewa. Saboda a ganin Sinawa, nuna fin karfi zai haddasa kiyayya da rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa. Dole ne a yi kokarin kare kai bisa adalci, da sauran tunani masu dacewa, sannan za a iya samun ingantaccen tsaro mai dorewa.

Wani abu mai faranta rai shi ne, yawancin kasashen duniya, ciki har da kasashen Afirka, sun yarda da shawarar kasar Sin, ganin yadda suke da ra’ayin tsaro iri daya da na kasar Sin. Bayan abkuwar yaki tsakanin kasar Rasha da ta Ukraine, kasashen Afirka da kasar Sin sun yi kokarin sulhuntawa don neman ganin Rasha da Ukraine sun tsagaita bude wuta da komawa teburin shawarwari. Haka kuma, bayan an yi juyin mulki a kasar Niger a wannan karo, nan take kasar Sin ta yi kira ga bangarori masu ruwa da tsaki na kasar Niger da su lura da moriyar kasar da ta al’ummarta, da daidaita rikici ta hanyar shawarwari. Kana a nata bangare, kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta tura shugaban kasar Benin, Patrice Talon, zuwa kasar Niger, don taimakawa daidaita yanayin da ake ciki a kasar.

Dole ne a zauna gaban teburi, domin a fara tattaunawa da shawarwari don neman daidaita rikici. Muna fatan ta wannan hanya za a iya daidaita rikicin siyasa da ya abku a kasar Niger cikin ruwan sanyi, kuma cikin sauri ba tare da wani jinkiri ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ECOWAS Na Duba Yiwuwar Amfani Da Karfin Soja Wajen Mayar Da Bazoum Kujera

Next Post

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Nada Wanda Zai Bincike CBN Da Sauran Hukumomin Kudi 

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

12 hours ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

13 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

15 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

17 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

17 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

1 day ago
Next Post
Yajin aiki: Tinubu Ya Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Dan Kara Masa Lokaci

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Nada Wanda Zai Bincike CBN Da Sauran Hukumomin Kudi 

LABARAI MASU NASABA

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.