ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima

by Sadiq
2 years ago
Shettima

Zababben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya yi watsi da jita-jitar da ake yadawa cewar shugaban kasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu yana kokarin Musuluntar da Nijeriya.

Ya bayyana haka ne a yayin wani taron lacca ta musamman da aka gudanar a Abuja ranar Asabar gabanin rantsar da sabuwar gwamnati.

  • Manomi Zai Iya Sayar Da Hatsinsa Kafin Ya Girbe?
  • Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP

“Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Musulmi ne wanda yake auren Kirista, ba wai Kirista kadai ba, amma fasto a Cocin Redeem.

ADVERTISEMENT

“Mutumin da bai Musuluntar da iyalinsa ba, mutane suna cewa yana son ya Musuluntar da kasa baki daya,” in ji Kashim Shettima.

Shettima ya kuma bayyana cewa a lokacin yana gwamnan Borno, akwai coci da dama da Boko Haram suka kone, bayan ya yi yunkurin gyaran cocin an ba shi shawara kada ya kuskura ya sake gina cocin.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

“Na shaida wa mutanen Borno cewa Kiristoci su ma suna da ruwa da tsaki a Nijeriya, ‘yan uwana ne maza da mata, na yi gaban kaina na sake gina wadannan coci-cocin,” in ji shi.

A yayin taron, Kashim Shettima ya bayyana cewa da gangan ya dauki dan kabilar Igbo kuma mai bin darikar Katolika domin ya zama shugaban masu tsaronsa.

Kazalika ya ce ya zabi Kirista daga arewacin Nijeriya domin ya zama dogarinsa don kara hadin kan kasa.

A lokacin da yake bayani, Kashim Shettima ya bukaci jami’an tsaron biyu su mike tsaye domin mutane su tabbatar da hakan inda aka yi ta tafi da sowa.

Tun kafin a gudanar da zaben 2023, an sha sukar Jam’iyyar APC mai mulki kan hadin da ta yi na Musulmi da Musulmi a matsayin wadanda za su yi takarar shugaban kasa da mataimaki inda ake cewa bai kamata ba domin Nijeriya ba ta Musulmai ba ce kadai.

Sai dai jam’iyyar ta sha kare zargin da ake yi mata inda ta rika jaddada cewa ta dauki matakin ne bisa cancanta ba addini ko yankin da mutanen suka fito ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin “Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani” A Turanci

An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin "Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani" A Turanci

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.