ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima

by Sadiq
3 years ago
Shettima

Zababben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya yi watsi da jita-jitar da ake yadawa cewar shugaban kasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu yana kokarin Musuluntar da Nijeriya.

Ya bayyana haka ne a yayin wani taron lacca ta musamman da aka gudanar a Abuja ranar Asabar gabanin rantsar da sabuwar gwamnati.

  • Manomi Zai Iya Sayar Da Hatsinsa Kafin Ya Girbe?
  • Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP

“Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Musulmi ne wanda yake auren Kirista, ba wai Kirista kadai ba, amma fasto a Cocin Redeem.

ADVERTISEMENT

“Mutumin da bai Musuluntar da iyalinsa ba, mutane suna cewa yana son ya Musuluntar da kasa baki daya,” in ji Kashim Shettima.

Shettima ya kuma bayyana cewa a lokacin yana gwamnan Borno, akwai coci da dama da Boko Haram suka kone, bayan ya yi yunkurin gyaran cocin an ba shi shawara kada ya kuskura ya sake gina cocin.

LABARAI MASU NASABA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

“Na shaida wa mutanen Borno cewa Kiristoci su ma suna da ruwa da tsaki a Nijeriya, ‘yan uwana ne maza da mata, na yi gaban kaina na sake gina wadannan coci-cocin,” in ji shi.

A yayin taron, Kashim Shettima ya bayyana cewa da gangan ya dauki dan kabilar Igbo kuma mai bin darikar Katolika domin ya zama shugaban masu tsaronsa.

Kazalika ya ce ya zabi Kirista daga arewacin Nijeriya domin ya zama dogarinsa don kara hadin kan kasa.

A lokacin da yake bayani, Kashim Shettima ya bukaci jami’an tsaron biyu su mike tsaye domin mutane su tabbatar da hakan inda aka yi ta tafi da sowa.

Tun kafin a gudanar da zaben 2023, an sha sukar Jam’iyyar APC mai mulki kan hadin da ta yi na Musulmi da Musulmi a matsayin wadanda za su yi takarar shugaban kasa da mataimaki inda ake cewa bai kamata ba domin Nijeriya ba ta Musulmai ba ce kadai.

Sai dai jam’iyyar ta sha kare zargin da ake yi mata inda ta rika jaddada cewa ta dauki matakin ne bisa cancanta ba addini ko yankin da mutanen suka fito ba.

MASU ALAKA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Next Post
An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin “Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani” A Turanci

An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin "Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani" A Turanci

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.