ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima

by Sadiq
3 years ago
Shettima

Zababben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya yi watsi da jita-jitar da ake yadawa cewar shugaban kasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu yana kokarin Musuluntar da Nijeriya.

Ya bayyana haka ne a yayin wani taron lacca ta musamman da aka gudanar a Abuja ranar Asabar gabanin rantsar da sabuwar gwamnati.

  • Manomi Zai Iya Sayar Da Hatsinsa Kafin Ya Girbe?
  • Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP

“Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Musulmi ne wanda yake auren Kirista, ba wai Kirista kadai ba, amma fasto a Cocin Redeem.

ADVERTISEMENT

“Mutumin da bai Musuluntar da iyalinsa ba, mutane suna cewa yana son ya Musuluntar da kasa baki daya,” in ji Kashim Shettima.

Shettima ya kuma bayyana cewa a lokacin yana gwamnan Borno, akwai coci da dama da Boko Haram suka kone, bayan ya yi yunkurin gyaran cocin an ba shi shawara kada ya kuskura ya sake gina cocin.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Na shaida wa mutanen Borno cewa Kiristoci su ma suna da ruwa da tsaki a Nijeriya, ‘yan uwana ne maza da mata, na yi gaban kaina na sake gina wadannan coci-cocin,” in ji shi.

A yayin taron, Kashim Shettima ya bayyana cewa da gangan ya dauki dan kabilar Igbo kuma mai bin darikar Katolika domin ya zama shugaban masu tsaronsa.

Kazalika ya ce ya zabi Kirista daga arewacin Nijeriya domin ya zama dogarinsa don kara hadin kan kasa.

A lokacin da yake bayani, Kashim Shettima ya bukaci jami’an tsaron biyu su mike tsaye domin mutane su tabbatar da hakan inda aka yi ta tafi da sowa.

Tun kafin a gudanar da zaben 2023, an sha sukar Jam’iyyar APC mai mulki kan hadin da ta yi na Musulmi da Musulmi a matsayin wadanda za su yi takarar shugaban kasa da mataimaki inda ake cewa bai kamata ba domin Nijeriya ba ta Musulmai ba ce kadai.

Sai dai jam’iyyar ta sha kare zargin da ake yi mata inda ta rika jaddada cewa ta dauki matakin ne bisa cancanta ba addini ko yankin da mutanen suka fito ba.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin “Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani” A Turanci

An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin "Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani" A Turanci

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.