ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida: AMDF Ta Nemi A Bai Wa ‘Yan Jarida Kariya A Afirka

by Sadiq
2 years ago
Jarida

Gidauniyar Ci Gaban Kafofin Watsa Labarai ta Afirka (AMDF), ta taya ‘yan jaridar Afirka murnar zagayowar ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta 2024.

Gidauniyar ta jaddada muhimmancin bai wa ‘yan jarida ‘yanci, mutuntawa da kuma riƙon amana.

  • WPFD 2024: Aikin Jarida A Yanayi Na Taɓarɓarewar Muhalli
  • ‘Gwamnatin Kano Da NNPP Sun Illata Siyasar Ganduje Duk Da Rashin Nasarar’

Wannan na cikin wata sanarwa da manajan kare ‘yancin ‘yan jarida na AMDF, Zhiroh Jatau, ya fitar a ranar Juma’a 3 ga watan Mayu, 2024.

ADVERTISEMENT

AMDF ta nuna irin muhimmanci da rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen tabbatar da ‘yanci, da riƙon amana.

Taken ranar na bana, “Rawar Da ‘Yan Jarida Ke Takawa A Duniya: Yadda Aikin Jarida Ke Tunkarar Rikicin Muhalli,” ranar ta jaddada rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen bayar da shawarwarin samar da yanayi mai inganci.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

Saboda haka gidauniyar ta jaddada muhimmancin fallasa kamfanoni da ƙungiyoyin da ke lalata albarkatun da ke doron ƙasa.

Wasu daga cikin matsalolin sun haɗa da sauyin yanayi, gurɓatar yanayi, da lalacewar hallitu, wanda gidauniyar ta bukaci ‘yan jarida su taka rawa wajen bayar da shawarwarin da za su kare muhalli daga gurɓacewa.

Gidauniyar ta ja hankali kan yiwuwar samun cin zarafin ‘yan jarida a ƙasashe irin su Ghana, Namibiya, Nijeriya, da Cape Verde, inda ake tsare ‘yan jarida, tare da kai wa kafafen watsa labarai samame sakamakon ayyukan da suke gudanarwa.

Abin takaici, yawancin ‘yan jaridar da ke bibiyar al’amuran da suka shafi cin hanci da rashawa a Afirka na fuskantar cin zarafi ta hanyar ɗauri da yi wa rayuwarsu barazana.

Saboda haka, AMDF ta yi kira ga hukumomin tsaro a Afrika da su ɗauki gaɓaren kare ‘yan jarida, tare da samar musu da yanayin da za su gudanar da ayyukansu cikin salama.

MASU ALAKA

Jarida
Labarai

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Jarida
Labarai

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Next Post
APC

Ba Mu Da Shirin Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya —APC

LABARAI MASU NASABA

Jarida

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Jarida

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Jarida

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Jarida

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.