ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Kama Emefiele Ba – DSS

by Sadiq
3 years ago
DSS

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), ta ce ba ta kai mamaya ofishin Babban Bankin Nijeriya ba kamar yadda wasu rahotanni suka nuna.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya ya fitar, ya kuma ce rundunar ‘yan sandan sirrin ba ta kama gwamnan CBN, Godwin Emefiele ba.

  • Musulman Sun Fusata Da Matakin Gwamnatin Bauchi Kan Makabarta
  • DSS Ta Karyata Yin Kawanya A Shalkwar CBN, Bayan Emefiele Ya Dawo Kan Aiki

Da yake karyata rahotannin da kafafen yada labarai suka yada na kama shi, kakakin DSS, ya bayyana hakan a matsayin labaran bogi.

ADVERTISEMENT

“An jawo hankalin Hukumar Tsaro Farin Kaya (DSS) kan labarin karya da ake yadawa cewa jami’anta sun mamaye Babban Bankin Nijeriya tare da kama gwamnansa, a yau 16/1/23. Wannan labari ne na karya kuma yaudara ce,” in ji sanarwar.

A halin yanzu dai Emefiele ya koma bakin aikinsa bayan hutun da ya yi a kasar waje.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Daraktan Sadarwa na CBN, Osita Nwanisobi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Litinin.

Sanarwar ta kara da cewa, “Gwamnan babban bankin ya koma aiki tare da sabunta kwarin guiwa don gudanar da aikinsa gabanin taron kwamitin kula da harkokin kudi na farko (MPC) na shekarar nan a ranar 23 zuwa 24 ga watan Janairu, 2023,” in ji sanarwar.

“Emefiele ya ci gaba da jajircewa wajen gudanar da aikin da ke gabansa daidai don tsarin manufofin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

A kwanakin baya ne dai DSS ta sanya wa Emefiele kahon zuka wanda suka kai kara kotu bisa zarginsa sa daukar nauyin ta’addanci.

DSS ta garzaya wata kotun Abuja domin samun sahalewa don ta kamo gwamnan babban bankin bisa zargin daukar nauyin ta’addanci da kuma laifukan da suka shafi tattalin arzikin kasa, amma mai shari’a Maryam Hassan ta babbar kotun, ta yi watsi da bukatar ta DSS.

Bayan haka, alkalin ta DSS kama, gayyata, ko tsare Emefiele, inda ta bayyana zargin ta’addancin da DSS ke yiwa gwamnan CBN a matsayin daukar zargi mara tushe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali

Akwai Hatsarin Gaske Mika Mulkin Nijeriya A Hannun Tinubu ko Obi - Atiku 

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.