• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Raba Ci Gaban Kasar Sin Da Gudunmuwar Mata Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ba Za A Raba Ci Gaban Kasar Sin Da Gudunmuwar Mata Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hadaddiyar kungiyar mata ta kasar Sin, da hukumar hadin gwiwar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar, sun kaddamar da wani sansanin ba da horo a fannin mu’amala, da hadin gwiwa ta fuskar samar da ci gaban harkokin mata na kasa da kasa. 

Hausawa kan ce ilmantar da mace guda, tamkar ilmantar da al’umma ne. Kamar yadda takwarorinsu maza suke taka rawa a harkokin da suka shafi shugabanci da tsara manufofi, su ma mata idan suka samu dama, za su iya bayar da kwatankwacin gudunmawar.

  • ‘Yan Kasuwar Afrika Sun Gano Zarafi Mai Kyau A Canton Fair
  • Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Baya ga tallafawa a bangarori kamar na bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa da sauransu, kasar Sin tana kuma mayar da hankali kan kowanne bangare da zai taimaka ga samar da ci gaba na bai daya, shi ya sa a ko da yaushe na kan bayyana ta a matsayin mai hangen nesa da kaifin basira. A zamana a kasar, na ga yadda ake bayar da muhimmanci ga harkokin mata da yadda ake ba su damarmaki daidai da takwarorinsu ba tare da nuna musu wariya ba. Kuma na ga yadda hakan ya ba mata damar taka rawa a fannoni daban-daban kama daga kimiyya da fasaha da tattalin arzikin da harkokin shugabanci da sauransu, har ma da yadda suka bayar da gudunmawa wajen fatattakar talauci, shi ya sa ba za a taba raba ci gaban da kasar Sin ta samu da gudunmawar mata ba.

Ina da yakinin cewa, rawar da mata a kasar Sin ke takawa sakamakon damarmakin da aka ba su ne ya sa kasar ke wa kasashe masu tasowa sha’awar irin hakan. Duk da cewa, an bar mata a baya cikin al’amuran da suka shafi tafiyar da harkokin kasashe da ma duniya, lokaci bai kure ba na damawa da su.

Ba shakka, wannan yunkuri na kungiyar mata ta kasar Sin da hukumar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar, ya bullo da kyakkyawar dabarar da za ta ba mata kwarin gwiwa, musamman na kasashenmu masu tasowa, ta yadda za su shiga a dama da su cikin muhimman harkokin kasa tare da bayar da irin nasu gudummawa ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasashensu. (Faeza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAmurkaUkraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Ma’aikata Albashi

Next Post

Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

Related

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
Daga Birnin Sin

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

10 hours ago
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

11 hours ago
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Daga Birnin Sin

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

13 hours ago
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

13 hours ago
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
Daga Birnin Sin

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

14 hours ago
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

15 hours ago
Next Post
Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.