• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Raba Ci Gaban Kasar Sin Da Gudunmuwar Mata Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ba Za A Raba Ci Gaban Kasar Sin Da Gudunmuwar Mata Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hadaddiyar kungiyar mata ta kasar Sin, da hukumar hadin gwiwar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar, sun kaddamar da wani sansanin ba da horo a fannin mu’amala, da hadin gwiwa ta fuskar samar da ci gaban harkokin mata na kasa da kasa. 

Hausawa kan ce ilmantar da mace guda, tamkar ilmantar da al’umma ne. Kamar yadda takwarorinsu maza suke taka rawa a harkokin da suka shafi shugabanci da tsara manufofi, su ma mata idan suka samu dama, za su iya bayar da kwatankwacin gudunmawar.

  • ‘Yan Kasuwar Afrika Sun Gano Zarafi Mai Kyau A Canton Fair
  • Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Baya ga tallafawa a bangarori kamar na bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa da sauransu, kasar Sin tana kuma mayar da hankali kan kowanne bangare da zai taimaka ga samar da ci gaba na bai daya, shi ya sa a ko da yaushe na kan bayyana ta a matsayin mai hangen nesa da kaifin basira. A zamana a kasar, na ga yadda ake bayar da muhimmanci ga harkokin mata da yadda ake ba su damarmaki daidai da takwarorinsu ba tare da nuna musu wariya ba. Kuma na ga yadda hakan ya ba mata damar taka rawa a fannoni daban-daban kama daga kimiyya da fasaha da tattalin arzikin da harkokin shugabanci da sauransu, har ma da yadda suka bayar da gudunmawa wajen fatattakar talauci, shi ya sa ba za a taba raba ci gaban da kasar Sin ta samu da gudunmawar mata ba.

Ina da yakinin cewa, rawar da mata a kasar Sin ke takawa sakamakon damarmakin da aka ba su ne ya sa kasar ke wa kasashe masu tasowa sha’awar irin hakan. Duk da cewa, an bar mata a baya cikin al’amuran da suka shafi tafiyar da harkokin kasashe da ma duniya, lokaci bai kure ba na damawa da su.

Ba shakka, wannan yunkuri na kungiyar mata ta kasar Sin da hukumar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar, ya bullo da kyakkyawar dabarar da za ta ba mata kwarin gwiwa, musamman na kasashenmu masu tasowa, ta yadda za su shiga a dama da su cikin muhimman harkokin kasa tare da bayar da irin nasu gudummawa ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasashensu. (Faeza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAmurkaUkraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Ma’aikata Albashi

Next Post

Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

Related

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

49 minutes ago
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

56 minutes ago
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

4 hours ago
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

23 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

1 day ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

1 day ago
Next Post
Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

Yan Sama Jannatin Shenzhou-17 Sun Dawo Doron Duniya

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.