• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Iya Zuba Kuɗina Masu Yawa A Yanzu In Yi Waƙa Ba -Adamu Nagudu

by Rabilu Sanusi Bena
9 months ago
in Nishadi
0
Ba Zan Iya Zuba Kuɗina Masu Yawa A Yanzu In Yi Waƙa Ba -Adamu Nagudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin manyan mawaka da suka yi tashe a shekarun baya a masana’antar Kannywood, Adamu Nagudu ya yi magana kan batutuwa da dama da suka hada da masana’antar Kannywood a da da yanzu da kuma sauran batutuwa da suka shafi rayuwarsa ta waka.

Nagudu a hirar da ya yi da jarumar Kannywood Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ya fara magana ne a kan yadda ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne a birnin Jos kafin ya dawo Kano da zama.

  • Burina Fim Ya Zama Sana’a A Nijeriya Kamar Indiya Da Amurka – Mustapha Nagudu
  • Karewar Basira A Wakokin Soyayya Ta Sa Na Daina Yin Su – Mahmud Nagudu

Inda ya ce Allah madaukakain Sarki shi ne kadai ya isa ya tsarawa dan adam yadda rayuwarshi za ta kasance, saboda haka ba abin mamaki ba ne ace malamin makarantar Islamiyya wanda ya ke da dalibai masu yawa a kasan shi daga baya kuma ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood, wannan iko ne na Allah kawai wanda yake abinda ya so ga wanda ya so a kuma lokacin da ya so.

Nagudu ya ci gaba da cewa a baya sunan shi Sayyadi wanda ya samu asali sakamakon karantar da kalibai da yake yi a Jos kafin ya zo Kano, amma bayan ya zo Kano sai ya fara aiki a wani kamfani da ake kira Nagudu Inbestment tare da abokina Mahmud Nagudu.

A kan tsohuwar alakar shi da jaruma Jamila Nagudu, Adamu ya ce a can baya tun kafin Jamila ta shigo harkar Kannywood muke tare da ita wanda har ya kai ga mun sako manya dangane da batun aurenmu, amma daga baya wasu suka hure mata kunne a kan a wancan lokacin tana da wata fuska ko lokaci da ya kamata ta fara harkar fim, hakan yasa ta ce ba za ta yi aure ba a wancan lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Da aka tambaye shi minene sirrin nasara ko daukakar da ya samu a masana’antar Kannywood, Adamu ya ce babu wani sirri akan wannan nasara da ya samu illa biyayya ga iyaye, domin kuwa a duk lokacin da iyayenka suka yi maka addu’ar samun nasar Insha Allah ba zaka wofanta ba muddin kana kyautata masu inji shi.

Adamu Nagudu ya ci gaba da cewa masana’antar Kannywood wadda ta ke da dadadden tarihi, ta canza matuka a bangaren tarbiyya da girmama juna a tsakanin jarumai a masana’antar ba kamar yadda muka yi a baya ba, domin a wancan lokacin akwai girmama juna a tsakanin manya da kanana a masana’antar ba kamar yanzu da zaka ga yaro yana nuna da shi da babba duk daya ne saboda dukansu mawaka ne ko kuma dukansu jaruman fim ne.

Haka kuma canjawar da Kannywood ta yi akwai ta barayin kasuwanci, domin a wancan lokacin idan ka saka kudadenka a masana’antar ta kowane fanni kama daga waka da masu shirya fina-finai, zaka samu riba matuka, ba kamar yanzu ba domin kuwa ni ba zan iya zuba kudadena a yanzu kamar yadda na zuba a lokacin baya ba in ji shi.

Daga karshe Adamu Nagudu ya ce ko alama bai yi da nasanin shigarsa masana’antar Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne kafin zuwansa Kannywood, domin kuwa babu abinda ya canza a matsayina na Malami kuma dalibi a makarantar Islamiyya, domin har yanzu duk ranar da Allah ya kaini Jos ni kan yi kokarin zuwa makarantar domin bayar da tawa gudunmawar a kowane fanni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilmKannywoodNaguduWaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Watsa Shirin Talabijin Na Labaran Gaskiya Mai Taken “Abokai Na Kusa Daga Dukkanin Nahiyoyi”

Next Post

Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

5 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon

Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu - Hadiza Gabon

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.