ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Iya Zuba Kuɗina Masu Yawa A Yanzu In Yi Waƙa Ba -Adamu Nagudu

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Nagudu

Daya daga cikin manyan mawaka da suka yi tashe a shekarun baya a masana’antar Kannywood, Adamu Nagudu ya yi magana kan batutuwa da dama da suka hada da masana’antar Kannywood a da da yanzu da kuma sauran batutuwa da suka shafi rayuwarsa ta waka.

Nagudu a hirar da ya yi da jarumar Kannywood Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ya fara magana ne a kan yadda ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne a birnin Jos kafin ya dawo Kano da zama.

  • Burina Fim Ya Zama Sana’a A Nijeriya Kamar Indiya Da Amurka – Mustapha Nagudu
  • Karewar Basira A Wakokin Soyayya Ta Sa Na Daina Yin Su – Mahmud Nagudu

Inda ya ce Allah madaukakain Sarki shi ne kadai ya isa ya tsarawa dan adam yadda rayuwarshi za ta kasance, saboda haka ba abin mamaki ba ne ace malamin makarantar Islamiyya wanda ya ke da dalibai masu yawa a kasan shi daga baya kuma ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood, wannan iko ne na Allah kawai wanda yake abinda ya so ga wanda ya so a kuma lokacin da ya so.

ADVERTISEMENT

Nagudu ya ci gaba da cewa a baya sunan shi Sayyadi wanda ya samu asali sakamakon karantar da kalibai da yake yi a Jos kafin ya zo Kano, amma bayan ya zo Kano sai ya fara aiki a wani kamfani da ake kira Nagudu Inbestment tare da abokina Mahmud Nagudu.

A kan tsohuwar alakar shi da jaruma Jamila Nagudu, Adamu ya ce a can baya tun kafin Jamila ta shigo harkar Kannywood muke tare da ita wanda har ya kai ga mun sako manya dangane da batun aurenmu, amma daga baya wasu suka hure mata kunne a kan a wancan lokacin tana da wata fuska ko lokaci da ya kamata ta fara harkar fim, hakan yasa ta ce ba za ta yi aure ba a wancan lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Da aka tambaye shi minene sirrin nasara ko daukakar da ya samu a masana’antar Kannywood, Adamu ya ce babu wani sirri akan wannan nasara da ya samu illa biyayya ga iyaye, domin kuwa a duk lokacin da iyayenka suka yi maka addu’ar samun nasar Insha Allah ba zaka wofanta ba muddin kana kyautata masu inji shi.

Adamu Nagudu ya ci gaba da cewa masana’antar Kannywood wadda ta ke da dadadden tarihi, ta canza matuka a bangaren tarbiyya da girmama juna a tsakanin jarumai a masana’antar ba kamar yadda muka yi a baya ba, domin a wancan lokacin akwai girmama juna a tsakanin manya da kanana a masana’antar ba kamar yanzu da zaka ga yaro yana nuna da shi da babba duk daya ne saboda dukansu mawaka ne ko kuma dukansu jaruman fim ne.

Haka kuma canjawar da Kannywood ta yi akwai ta barayin kasuwanci, domin a wancan lokacin idan ka saka kudadenka a masana’antar ta kowane fanni kama daga waka da masu shirya fina-finai, zaka samu riba matuka, ba kamar yanzu ba domin kuwa ni ba zan iya zuba kudadena a yanzu kamar yadda na zuba a lokacin baya ba in ji shi.

Daga karshe Adamu Nagudu ya ce ko alama bai yi da nasanin shigarsa masana’antar Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne kafin zuwansa Kannywood, domin kuwa babu abinda ya canza a matsayina na Malami kuma dalibi a makarantar Islamiyya, domin har yanzu duk ranar da Allah ya kaini Jos ni kan yi kokarin zuwa makarantar domin bayar da tawa gudunmawar a kowane fanni.

Nagudu
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon

Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu - Hadiza Gabon

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.