ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Iya Zuba Kuɗina Masu Yawa A Yanzu In Yi Waƙa Ba -Adamu Nagudu

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Nagudu

Daya daga cikin manyan mawaka da suka yi tashe a shekarun baya a masana’antar Kannywood, Adamu Nagudu ya yi magana kan batutuwa da dama da suka hada da masana’antar Kannywood a da da yanzu da kuma sauran batutuwa da suka shafi rayuwarsa ta waka.

Nagudu a hirar da ya yi da jarumar Kannywood Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ya fara magana ne a kan yadda ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne a birnin Jos kafin ya dawo Kano da zama.

  • Burina Fim Ya Zama Sana’a A Nijeriya Kamar Indiya Da Amurka – Mustapha Nagudu
  • Karewar Basira A Wakokin Soyayya Ta Sa Na Daina Yin Su – Mahmud Nagudu

Inda ya ce Allah madaukakain Sarki shi ne kadai ya isa ya tsarawa dan adam yadda rayuwarshi za ta kasance, saboda haka ba abin mamaki ba ne ace malamin makarantar Islamiyya wanda ya ke da dalibai masu yawa a kasan shi daga baya kuma ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood, wannan iko ne na Allah kawai wanda yake abinda ya so ga wanda ya so a kuma lokacin da ya so.

ADVERTISEMENT

Nagudu ya ci gaba da cewa a baya sunan shi Sayyadi wanda ya samu asali sakamakon karantar da kalibai da yake yi a Jos kafin ya zo Kano, amma bayan ya zo Kano sai ya fara aiki a wani kamfani da ake kira Nagudu Inbestment tare da abokina Mahmud Nagudu.

A kan tsohuwar alakar shi da jaruma Jamila Nagudu, Adamu ya ce a can baya tun kafin Jamila ta shigo harkar Kannywood muke tare da ita wanda har ya kai ga mun sako manya dangane da batun aurenmu, amma daga baya wasu suka hure mata kunne a kan a wancan lokacin tana da wata fuska ko lokaci da ya kamata ta fara harkar fim, hakan yasa ta ce ba za ta yi aure ba a wancan lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Da aka tambaye shi minene sirrin nasara ko daukakar da ya samu a masana’antar Kannywood, Adamu ya ce babu wani sirri akan wannan nasara da ya samu illa biyayya ga iyaye, domin kuwa a duk lokacin da iyayenka suka yi maka addu’ar samun nasar Insha Allah ba zaka wofanta ba muddin kana kyautata masu inji shi.

Adamu Nagudu ya ci gaba da cewa masana’antar Kannywood wadda ta ke da dadadden tarihi, ta canza matuka a bangaren tarbiyya da girmama juna a tsakanin jarumai a masana’antar ba kamar yadda muka yi a baya ba, domin a wancan lokacin akwai girmama juna a tsakanin manya da kanana a masana’antar ba kamar yanzu da zaka ga yaro yana nuna da shi da babba duk daya ne saboda dukansu mawaka ne ko kuma dukansu jaruman fim ne.

Haka kuma canjawar da Kannywood ta yi akwai ta barayin kasuwanci, domin a wancan lokacin idan ka saka kudadenka a masana’antar ta kowane fanni kama daga waka da masu shirya fina-finai, zaka samu riba matuka, ba kamar yanzu ba domin kuwa ni ba zan iya zuba kudadena a yanzu kamar yadda na zuba a lokacin baya ba in ji shi.

Daga karshe Adamu Nagudu ya ce ko alama bai yi da nasanin shigarsa masana’antar Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne kafin zuwansa Kannywood, domin kuwa babu abinda ya canza a matsayina na Malami kuma dalibi a makarantar Islamiyya, domin har yanzu duk ranar da Allah ya kaini Jos ni kan yi kokarin zuwa makarantar domin bayar da tawa gudunmawar a kowane fanni.

Nagudu
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon

Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu - Hadiza Gabon

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.