ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Iya Zuba Kuɗina Masu Yawa A Yanzu In Yi Waƙa Ba -Adamu Nagudu

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Nagudu

Daya daga cikin manyan mawaka da suka yi tashe a shekarun baya a masana’antar Kannywood, Adamu Nagudu ya yi magana kan batutuwa da dama da suka hada da masana’antar Kannywood a da da yanzu da kuma sauran batutuwa da suka shafi rayuwarsa ta waka.

Nagudu a hirar da ya yi da jarumar Kannywood Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’ ya fara magana ne a kan yadda ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne a birnin Jos kafin ya dawo Kano da zama.

  • Burina Fim Ya Zama Sana’a A Nijeriya Kamar Indiya Da Amurka – Mustapha Nagudu
  • Karewar Basira A Wakokin Soyayya Ta Sa Na Daina Yin Su – Mahmud Nagudu

Inda ya ce Allah madaukakain Sarki shi ne kadai ya isa ya tsarawa dan adam yadda rayuwarshi za ta kasance, saboda haka ba abin mamaki ba ne ace malamin makarantar Islamiyya wanda ya ke da dalibai masu yawa a kasan shi daga baya kuma ya samu kanshi a matsayin mawakin Kannywood, wannan iko ne na Allah kawai wanda yake abinda ya so ga wanda ya so a kuma lokacin da ya so.

ADVERTISEMENT

Nagudu ya ci gaba da cewa a baya sunan shi Sayyadi wanda ya samu asali sakamakon karantar da kalibai da yake yi a Jos kafin ya zo Kano, amma bayan ya zo Kano sai ya fara aiki a wani kamfani da ake kira Nagudu Inbestment tare da abokina Mahmud Nagudu.

A kan tsohuwar alakar shi da jaruma Jamila Nagudu, Adamu ya ce a can baya tun kafin Jamila ta shigo harkar Kannywood muke tare da ita wanda har ya kai ga mun sako manya dangane da batun aurenmu, amma daga baya wasu suka hure mata kunne a kan a wancan lokacin tana da wata fuska ko lokaci da ya kamata ta fara harkar fim, hakan yasa ta ce ba za ta yi aure ba a wancan lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Da aka tambaye shi minene sirrin nasara ko daukakar da ya samu a masana’antar Kannywood, Adamu ya ce babu wani sirri akan wannan nasara da ya samu illa biyayya ga iyaye, domin kuwa a duk lokacin da iyayenka suka yi maka addu’ar samun nasar Insha Allah ba zaka wofanta ba muddin kana kyautata masu inji shi.

Adamu Nagudu ya ci gaba da cewa masana’antar Kannywood wadda ta ke da dadadden tarihi, ta canza matuka a bangaren tarbiyya da girmama juna a tsakanin jarumai a masana’antar ba kamar yadda muka yi a baya ba, domin a wancan lokacin akwai girmama juna a tsakanin manya da kanana a masana’antar ba kamar yanzu da zaka ga yaro yana nuna da shi da babba duk daya ne saboda dukansu mawaka ne ko kuma dukansu jaruman fim ne.

Haka kuma canjawar da Kannywood ta yi akwai ta barayin kasuwanci, domin a wancan lokacin idan ka saka kudadenka a masana’antar ta kowane fanni kama daga waka da masu shirya fina-finai, zaka samu riba matuka, ba kamar yanzu ba domin kuwa ni ba zan iya zuba kudadena a yanzu kamar yadda na zuba a lokacin baya ba in ji shi.

Daga karshe Adamu Nagudu ya ce ko alama bai yi da nasanin shigarsa masana’antar Kannywood duk da cewar shi malamin makarantar Islamiyya ne kafin zuwansa Kannywood, domin kuwa babu abinda ya canza a matsayina na Malami kuma dalibi a makarantar Islamiyya, domin har yanzu duk ranar da Allah ya kaini Jos ni kan yi kokarin zuwa makarantar domin bayar da tawa gudunmawar a kowane fanni.

Nagudu
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu – Hadiza Gabon

Masu Sa Hotona A Soshiyal Midiya Suna Yabo Babu Abin Da Za Su Samu - Hadiza Gabon

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.