An bayyana ce wa samun yarinya mai shekaru 6 a duniya ta haddace alkur’ani a makarantar Raudatul Jannah Tahfizul kur’an International School da ke Rangaza a karamar hukumar Ungoggo a karkashin shugabancin Imam Muhammad Yakub, babban al’amari ne ga Jihar Kano dama Nijeriya.
Kamar yadda Alhaji Mustapha Garba Mai Sikeli, tsohon dan jarida, ya bayyana hakan a matsayinsa na babban bako a walimar yaye daliban makarantar Raudatul Jannah Rangaza Kano
- Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo
- Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido
Ya yi kira ga shigabanni da kungiyoyi su rika hada kai da hukumomi masu kula da kirkira da fasahar yara kanana da ke karkashin kwamishinan ma’aikatar kimiya da fasaha na Jihar Kano da sauran hukumomin jihar dama na Nijeriya.
A jawabinsa, shugaban makarantar, Imam Muhammad Yakub ya ce abu ne na Allah, b
a karfinsu ba ne, ba na iyawarsu ba ne, Allah ne ya yarda kuma ba abun da ya gagari Ubangiji a akida ta Musulinci, ana dai bukatar duk abun da Musulmi zai yi ya sa tsoron Allah.
Ya kara da cewa wannan sauka ita ce karo na hudu wanda aka yi walimar dalibai 45, maza da mata, inda mafi kankanta daliba ita ce mai shekaru shida da rabi da makarantar ta yaye jimlar dalibai 90 kenan tun daga 2018 zuwa wannan shekara 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp