• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023

•Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Mai Shara’a na Kasa, Justice Olukayode Ariwoola ya gargadi alkalan da aka ware domin jin korafe-korafen zaben 2023 su gudanar da gaskiya da amana wajen zantar da hukunci a kasa kar su kuskura su ci amanan ‘yan Nijeriya a 2023.

Babban mai shari’a na kasa ya bayyana hakan ne a lokacin bude taron bita na kwanaki hadu da aka shirya wa alkalan da za su saurari korafe-korafen zabe a cibiyar shari’a ta kasa da ke Abuja a ranar Litinin da ta gabata.

  • Kotu Ta Kori Sanatan Taraba Daga Kujerarsa Saboda Sauya Sheka Zuwa APC 

Justice Ariwoola ya bukaci jami’an da ke sashin shari’a da su cire duk wata son zuciya wajen gudanar da harkokin shari’a a lokacin da suke yanke hukunci kan a kotuna.
“Ya kamata alkalai su zama masu gaskiya da rukon amana a lokacin da suke zantar da hukunci kan wadanda suka tsaya takara a mukamai daban-daban a zaben 2023, domin su ne masu kwato wa wadanda ba a yi musu adalci ba hakkinsu, sannan ya zama wajibi su yi kokarin sauke nauyin da Allah ya daura musu cikin gaskiya da rikon amana.

“Ba a bukatar jami’an da ke sashin shari’a su kasance masu rashin gaskiya wajen gudanar da ayyukansu da ka daura musu, ina mai tabbatar muku da cewa al’umma suna da matukar kwarin gwiwa a kanku wajen yi musu adalci lokacin sauraran karar zabe.
“Gaskiya nauyi ne da ya rataya a wuyanku lokacin da kuke gudanar da ayyukanku na alkalanci, saboda ku kuke amso wa mara karfi hakkinsa ta hanyar gaskiya.

“Dole ku tashi tsaye wajen yakar son zuciya a wurin gudanar da ayyukanku na alkalanci, musamman wajen sauraren korafe-korafen zabe,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Haka ita ma shugaban kotun daukaka kara, Justice Monica Dongban-Mensem ta bayyana cewa alkalan guda 277 wadanda aka zabe domin sauraron korafe-korafen zabe wadanda suka hada da na babban kotun tarayya 4 da kotun sauraron karar ma’aikata ta kasa 3 da na babban kotun Abuja da na jihohi 213 da kotun gargajiya 13 da kotun shari’ar Musulunci 27 da kuma kotun majastiri 17.

Ta bukaci alkalan da su yi kokarin gudanar da aiki bisa kwarewarsu wajen sauke nauyin da aka daura musu.

Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC
A nasa jawabin, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta na kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa a yanzu haka hukumarsa ta shigar da kara 600 daga zaben fid da gwani na jam’iyyun siyasa daban-daban da suka gudanar domin shiga zaben 2023.

Ya kara da cewa hukumarsa ta yi nazarin kan hukunce-hukuncen zaben 2019, musamman wadanda suke kewaye da zabukan gwamnoni da zabukan cike gurbi da aka kammala a wasu yankun wadanda suke bukatar kai kara.

“Cikin makonni biyu da suka gabata, jam’iyya daya kacal mun samu korafi har guda 70 wadanda muka shigar a kotu a cikin mako daya da ke neman amincewa ko sauya ‘yan takara bayan wa’adin da muka saka kan jaddawalin zaben 2023 ya kare.
“An dai kai wasu korafe-korafen zuwa kotun koli,” in ji shi.

Ya zayyano yadda aka samu nasarori a cikin dokar zaben 2022 wanda aka inganta babban zaben 2023, musamman ma samar da na’urorin bayyana sakamakon zabe da hukumar zabe za ta samu nasarar cike gibi a tsakanin dokar zaben 2010.

“Haka kuma, sabon dokar zabe ta bayar da damar shigar da hurimin sauraron kararrakin korafe-korafin gabanin zabe a babban kotun tarayya kan zaben ‘yan takara domin a rage cinkoson a bangaren doka da kuma yin amfani da kotuna ba bisa ka’ida ba wajen yanke hukuncin kan hurumin da kotuna suke da shi,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kurar Sauya Fasalin Kudi: ‘Mahaukatan’ Sayen-sayen Da Masu Boye Kudi Ke Yi

Next Post

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.