• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023

•Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Mai Shara’a na Kasa, Justice Olukayode Ariwoola ya gargadi alkalan da aka ware domin jin korafe-korafen zaben 2023 su gudanar da gaskiya da amana wajen zantar da hukunci a kasa kar su kuskura su ci amanan ‘yan Nijeriya a 2023.

Babban mai shari’a na kasa ya bayyana hakan ne a lokacin bude taron bita na kwanaki hadu da aka shirya wa alkalan da za su saurari korafe-korafen zabe a cibiyar shari’a ta kasa da ke Abuja a ranar Litinin da ta gabata.

  • Kotu Ta Kori Sanatan Taraba Daga Kujerarsa Saboda Sauya Sheka Zuwa APC 

Justice Ariwoola ya bukaci jami’an da ke sashin shari’a da su cire duk wata son zuciya wajen gudanar da harkokin shari’a a lokacin da suke yanke hukunci kan a kotuna.
“Ya kamata alkalai su zama masu gaskiya da rukon amana a lokacin da suke zantar da hukunci kan wadanda suka tsaya takara a mukamai daban-daban a zaben 2023, domin su ne masu kwato wa wadanda ba a yi musu adalci ba hakkinsu, sannan ya zama wajibi su yi kokarin sauke nauyin da Allah ya daura musu cikin gaskiya da rikon amana.

“Ba a bukatar jami’an da ke sashin shari’a su kasance masu rashin gaskiya wajen gudanar da ayyukansu da ka daura musu, ina mai tabbatar muku da cewa al’umma suna da matukar kwarin gwiwa a kanku wajen yi musu adalci lokacin sauraran karar zabe.
“Gaskiya nauyi ne da ya rataya a wuyanku lokacin da kuke gudanar da ayyukanku na alkalanci, saboda ku kuke amso wa mara karfi hakkinsa ta hanyar gaskiya.

“Dole ku tashi tsaye wajen yakar son zuciya a wurin gudanar da ayyukanku na alkalanci, musamman wajen sauraren korafe-korafen zabe,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Haka ita ma shugaban kotun daukaka kara, Justice Monica Dongban-Mensem ta bayyana cewa alkalan guda 277 wadanda aka zabe domin sauraron korafe-korafen zabe wadanda suka hada da na babban kotun tarayya 4 da kotun sauraron karar ma’aikata ta kasa 3 da na babban kotun Abuja da na jihohi 213 da kotun gargajiya 13 da kotun shari’ar Musulunci 27 da kuma kotun majastiri 17.

Ta bukaci alkalan da su yi kokarin gudanar da aiki bisa kwarewarsu wajen sauke nauyin da aka daura musu.

Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC
A nasa jawabin, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta na kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa a yanzu haka hukumarsa ta shigar da kara 600 daga zaben fid da gwani na jam’iyyun siyasa daban-daban da suka gudanar domin shiga zaben 2023.

Ya kara da cewa hukumarsa ta yi nazarin kan hukunce-hukuncen zaben 2019, musamman wadanda suke kewaye da zabukan gwamnoni da zabukan cike gurbi da aka kammala a wasu yankun wadanda suke bukatar kai kara.

“Cikin makonni biyu da suka gabata, jam’iyya daya kacal mun samu korafi har guda 70 wadanda muka shigar a kotu a cikin mako daya da ke neman amincewa ko sauya ‘yan takara bayan wa’adin da muka saka kan jaddawalin zaben 2023 ya kare.
“An dai kai wasu korafe-korafen zuwa kotun koli,” in ji shi.

Ya zayyano yadda aka samu nasarori a cikin dokar zaben 2022 wanda aka inganta babban zaben 2023, musamman ma samar da na’urorin bayyana sakamakon zabe da hukumar zabe za ta samu nasarar cike gibi a tsakanin dokar zaben 2010.

“Haka kuma, sabon dokar zabe ta bayar da damar shigar da hurimin sauraron kararrakin korafe-korafin gabanin zabe a babban kotun tarayya kan zaben ‘yan takara domin a rage cinkoson a bangaren doka da kuma yin amfani da kotuna ba bisa ka’ida ba wajen yanke hukuncin kan hurumin da kotuna suke da shi,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kurar Sauya Fasalin Kudi: ‘Mahaukatan’ Sayen-sayen Da Masu Boye Kudi Ke Yi

Next Post

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.