• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Sufeton ‘Yansanda Ya Gargadi Masu Shirin Kawo Cikas Ga Mika Mulki

by Bello Hamza
2 years ago
Sufeton

A yayin da ranar 29 ga watan Mayu ke kara karatowa, ranar da za a rantsar da shugaban tarayyar Nijeriya da sauran zababbun gwamnoni a fadin tarayya kasa, Babban sufeton ‘yansanda Nijeriya IGP Usman Baba ya ja kunnen ‘yan siyasa da sauran masu barazanar kawo wa ranar dimokradiyyar kasa cikas.

Babban sufeton ya yi wannan gargadi ne a taron manema labarai da ya kira a ofishinsa da ke Abuja, ya ce, rundunar ‘yansanda ba za su zura ido ba ana yi wa shirin kaddamar da da sabuwar gwamnati barazana.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Da Dumi-dumi: ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Yin Garkuwa Da ‘Yan Hidimar Kasa A Jihar Ribas

Ya ce,, “Ba za a iya kiyasta bukata da muhimmancin zaman lafiya a rayuwar mu ta yau da kullum a Nijeriya ba, musamman bukatar tabbatar da tsaro a daidai wannan lokaci na rayuwar kasar mu Nijerriya, a saboda haka rundunar ‘yansanda na aiki tare da dukkan jami’an tsaro a Nijeriya, za kuma mu ci gaba da sanya ido a kan tsirarun ‘yansiyasa masu shirin tayar da fitina a kan haka muke kira gare su da su shiga taitayinsu, don ba za a lamunce musu ba..

“Da farko, rundunar ‘yansandan Nijeriya na gargadi ga dukkan ‘yan siyasa masu son tayar da zaune tsaye da masu goya musu baya, musamman ‘yan bangan su da suke turawa gaba-gaba da su gaggauta janye mugun shirinsu, su kuma sani cewa, furuce-furucen su na tayar da hankulan al’umma adai-dai lokacin da ake shirye-shiryen bukukuwan mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

“Na biyu kuma duk wani mahaluki ba tare da nuna banbancin a wacce jam’iyyar siyasa ko kungiya yake da ya ci gaba da harkokin da za su iya kawo cikas ga shirin ranstar da sabuwar gwamnati ko kuma barazana ga zaman lafiyar al’umma, tabbas rundunar ‘yansanda za su dakile shi ba tare da saurarawa ba, don kuwa mun shirya aiki da dukkan rundunonin tsaro wajen tabbatar da shirin rantsar da sabuwar gamnati bai samu wata matsala ba.

LABARAI MASU NASABA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

“Na uku, ya kamata al’umma su fahimci cewa, rantsar da sabuwar gwamnati a dukkan mataki abu ne da ya shafi kundin tsasrin mulkin Nijeriya, a kan haka rundunar ‘yansanda na da hakkin ganin ta kare duk wani abin da ke tare da tsarin mulkin Nijeriya, za kuma mu tabbatar da kare tsarin mulkin Nijeriya kamar yadda muka yi rantsuwar haka tun a farkon kama aikimu.

“A kan haka nike sanar da al’umam Nijeriya cewa, muna nan a kan shirin mu na kare dukkan kundin tsarin mulkin Nijeriya ba tare da ja da baya ba.. Za mu kare dimokradiyya a dukkan mataki. Za mu tabbatar da an kare ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da shugaban tayayyar Nijeriya da sauran wadanda za a rantsar a fadin Nijeriya a cikin kwanciyar hankali kamar yadda aka shirya.”

Ya kuma bukaci al’umma kasashen duniya su kaucewa dukkan ayyukan da zai iya haifar da barazana ga wannan rana ta hanyar yin wasu furuce-furice a kafafen sadarwa na zaman ida za su iya harfar da tashin hankali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAWIA
Labarai

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Next Post
An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.