• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Sufeton ‘Yansanda Ya Gargadi Masu Shirin Kawo Cikas Ga Mika Mulki

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Babban Sufeton ‘Yansanda Ya Gargadi Masu Shirin Kawo Cikas Ga Mika Mulki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ranar 29 ga watan Mayu ke kara karatowa, ranar da za a rantsar da shugaban tarayyar Nijeriya da sauran zababbun gwamnoni a fadin tarayya kasa, Babban sufeton ‘yansanda Nijeriya IGP Usman Baba ya ja kunnen ‘yan siyasa da sauran masu barazanar kawo wa ranar dimokradiyyar kasa cikas.

Babban sufeton ya yi wannan gargadi ne a taron manema labarai da ya kira a ofishinsa da ke Abuja, ya ce, rundunar ‘yansanda ba za su zura ido ba ana yi wa shirin kaddamar da da sabuwar gwamnati barazana.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Da Dumi-dumi: ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Yin Garkuwa Da ‘Yan Hidimar Kasa A Jihar Ribas

Ya ce,, “Ba za a iya kiyasta bukata da muhimmancin zaman lafiya a rayuwar mu ta yau da kullum a Nijeriya ba, musamman bukatar tabbatar da tsaro a daidai wannan lokaci na rayuwar kasar mu Nijerriya, a saboda haka rundunar ‘yansanda na aiki tare da dukkan jami’an tsaro a Nijeriya, za kuma mu ci gaba da sanya ido a kan tsirarun ‘yansiyasa masu shirin tayar da fitina a kan haka muke kira gare su da su shiga taitayinsu, don ba za a lamunce musu ba..

“Da farko, rundunar ‘yansandan Nijeriya na gargadi ga dukkan ‘yan siyasa masu son tayar da zaune tsaye da masu goya musu baya, musamman ‘yan bangan su da suke turawa gaba-gaba da su gaggauta janye mugun shirinsu, su kuma sani cewa, furuce-furucen su na tayar da hankulan al’umma adai-dai lokacin da ake shirye-shiryen bukukuwan mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

“Na biyu kuma duk wani mahaluki ba tare da nuna banbancin a wacce jam’iyyar siyasa ko kungiya yake da ya ci gaba da harkokin da za su iya kawo cikas ga shirin ranstar da sabuwar gwamnati ko kuma barazana ga zaman lafiyar al’umma, tabbas rundunar ‘yansanda za su dakile shi ba tare da saurarawa ba, don kuwa mun shirya aiki da dukkan rundunonin tsaro wajen tabbatar da shirin rantsar da sabuwar gamnati bai samu wata matsala ba.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

“Na uku, ya kamata al’umma su fahimci cewa, rantsar da sabuwar gwamnati a dukkan mataki abu ne da ya shafi kundin tsasrin mulkin Nijeriya, a kan haka rundunar ‘yansanda na da hakkin ganin ta kare duk wani abin da ke tare da tsarin mulkin Nijeriya, za kuma mu tabbatar da kare tsarin mulkin Nijeriya kamar yadda muka yi rantsuwar haka tun a farkon kama aikimu.

“A kan haka nike sanar da al’umam Nijeriya cewa, muna nan a kan shirin mu na kare dukkan kundin tsarin mulkin Nijeriya ba tare da ja da baya ba.. Za mu kare dimokradiyya a dukkan mataki. Za mu tabbatar da an kare ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da shugaban tayayyar Nijeriya da sauran wadanda za a rantsar a fadin Nijeriya a cikin kwanciyar hankali kamar yadda aka shirya.”

Ya kuma bukaci al’umma kasashen duniya su kaucewa dukkan ayyukan da zai iya haifar da barazana ga wannan rana ta hanyar yin wasu furuce-furice a kafafen sadarwa na zaman ida za su iya harfar da tashin hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargadiMika MulkiSufeton 'Yansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Next Post

An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

2 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

3 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

4 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

5 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

6 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

7 hours ago
Next Post
An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.