ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Sufeton ‘Yansanda Ya Gargadi Masu Shirin Kawo Cikas Ga Mika Mulki

by Bello Hamza
3 years ago
Sufeton

A yayin da ranar 29 ga watan Mayu ke kara karatowa, ranar da za a rantsar da shugaban tarayyar Nijeriya da sauran zababbun gwamnoni a fadin tarayya kasa, Babban sufeton ‘yansanda Nijeriya IGP Usman Baba ya ja kunnen ‘yan siyasa da sauran masu barazanar kawo wa ranar dimokradiyyar kasa cikas.

Babban sufeton ya yi wannan gargadi ne a taron manema labarai da ya kira a ofishinsa da ke Abuja, ya ce, rundunar ‘yansanda ba za su zura ido ba ana yi wa shirin kaddamar da da sabuwar gwamnati barazana.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Da Dumi-dumi: ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Yin Garkuwa Da ‘Yan Hidimar Kasa A Jihar Ribas

Ya ce,, “Ba za a iya kiyasta bukata da muhimmancin zaman lafiya a rayuwar mu ta yau da kullum a Nijeriya ba, musamman bukatar tabbatar da tsaro a daidai wannan lokaci na rayuwar kasar mu Nijerriya, a saboda haka rundunar ‘yansanda na aiki tare da dukkan jami’an tsaro a Nijeriya, za kuma mu ci gaba da sanya ido a kan tsirarun ‘yansiyasa masu shirin tayar da fitina a kan haka muke kira gare su da su shiga taitayinsu, don ba za a lamunce musu ba..

ADVERTISEMENT

“Da farko, rundunar ‘yansandan Nijeriya na gargadi ga dukkan ‘yan siyasa masu son tayar da zaune tsaye da masu goya musu baya, musamman ‘yan bangan su da suke turawa gaba-gaba da su gaggauta janye mugun shirinsu, su kuma sani cewa, furuce-furucen su na tayar da hankulan al’umma adai-dai lokacin da ake shirye-shiryen bukukuwan mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

“Na biyu kuma duk wani mahaluki ba tare da nuna banbancin a wacce jam’iyyar siyasa ko kungiya yake da ya ci gaba da harkokin da za su iya kawo cikas ga shirin ranstar da sabuwar gwamnati ko kuma barazana ga zaman lafiyar al’umma, tabbas rundunar ‘yansanda za su dakile shi ba tare da saurarawa ba, don kuwa mun shirya aiki da dukkan rundunonin tsaro wajen tabbatar da shirin rantsar da sabuwar gamnati bai samu wata matsala ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

“Na uku, ya kamata al’umma su fahimci cewa, rantsar da sabuwar gwamnati a dukkan mataki abu ne da ya shafi kundin tsasrin mulkin Nijeriya, a kan haka rundunar ‘yansanda na da hakkin ganin ta kare duk wani abin da ke tare da tsarin mulkin Nijeriya, za kuma mu tabbatar da kare tsarin mulkin Nijeriya kamar yadda muka yi rantsuwar haka tun a farkon kama aikimu.

“A kan haka nike sanar da al’umam Nijeriya cewa, muna nan a kan shirin mu na kare dukkan kundin tsarin mulkin Nijeriya ba tare da ja da baya ba.. Za mu kare dimokradiyya a dukkan mataki. Za mu tabbatar da an kare ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da shugaban tayayyar Nijeriya da sauran wadanda za a rantsar a fadin Nijeriya a cikin kwanciyar hankali kamar yadda aka shirya.”

Ya kuma bukaci al’umma kasashen duniya su kaucewa dukkan ayyukan da zai iya haifar da barazana ga wannan rana ta hanyar yin wasu furuce-furice a kafafen sadarwa na zaman ida za su iya harfar da tashin hankali.

Sufeton
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.