ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Sufeton ‘Yansanda Ya Gargadi Masu Shirin Kawo Cikas Ga Mika Mulki

by Bello Hamza
3 years ago
Sufeton

A yayin da ranar 29 ga watan Mayu ke kara karatowa, ranar da za a rantsar da shugaban tarayyar Nijeriya da sauran zababbun gwamnoni a fadin tarayya kasa, Babban sufeton ‘yansanda Nijeriya IGP Usman Baba ya ja kunnen ‘yan siyasa da sauran masu barazanar kawo wa ranar dimokradiyyar kasa cikas.

Babban sufeton ya yi wannan gargadi ne a taron manema labarai da ya kira a ofishinsa da ke Abuja, ya ce, rundunar ‘yansanda ba za su zura ido ba ana yi wa shirin kaddamar da da sabuwar gwamnati barazana.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Da Dumi-dumi: ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Yin Garkuwa Da ‘Yan Hidimar Kasa A Jihar Ribas

Ya ce,, “Ba za a iya kiyasta bukata da muhimmancin zaman lafiya a rayuwar mu ta yau da kullum a Nijeriya ba, musamman bukatar tabbatar da tsaro a daidai wannan lokaci na rayuwar kasar mu Nijerriya, a saboda haka rundunar ‘yansanda na aiki tare da dukkan jami’an tsaro a Nijeriya, za kuma mu ci gaba da sanya ido a kan tsirarun ‘yansiyasa masu shirin tayar da fitina a kan haka muke kira gare su da su shiga taitayinsu, don ba za a lamunce musu ba..

ADVERTISEMENT

“Da farko, rundunar ‘yansandan Nijeriya na gargadi ga dukkan ‘yan siyasa masu son tayar da zaune tsaye da masu goya musu baya, musamman ‘yan bangan su da suke turawa gaba-gaba da su gaggauta janye mugun shirinsu, su kuma sani cewa, furuce-furucen su na tayar da hankulan al’umma adai-dai lokacin da ake shirye-shiryen bukukuwan mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

“Na biyu kuma duk wani mahaluki ba tare da nuna banbancin a wacce jam’iyyar siyasa ko kungiya yake da ya ci gaba da harkokin da za su iya kawo cikas ga shirin ranstar da sabuwar gwamnati ko kuma barazana ga zaman lafiyar al’umma, tabbas rundunar ‘yansanda za su dakile shi ba tare da saurarawa ba, don kuwa mun shirya aiki da dukkan rundunonin tsaro wajen tabbatar da shirin rantsar da sabuwar gamnati bai samu wata matsala ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

“Na uku, ya kamata al’umma su fahimci cewa, rantsar da sabuwar gwamnati a dukkan mataki abu ne da ya shafi kundin tsasrin mulkin Nijeriya, a kan haka rundunar ‘yansanda na da hakkin ganin ta kare duk wani abin da ke tare da tsarin mulkin Nijeriya, za kuma mu tabbatar da kare tsarin mulkin Nijeriya kamar yadda muka yi rantsuwar haka tun a farkon kama aikimu.

“A kan haka nike sanar da al’umam Nijeriya cewa, muna nan a kan shirin mu na kare dukkan kundin tsarin mulkin Nijeriya ba tare da ja da baya ba.. Za mu kare dimokradiyya a dukkan mataki. Za mu tabbatar da an kare ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da shugaban tayayyar Nijeriya da sauran wadanda za a rantsar a fadin Nijeriya a cikin kwanciyar hankali kamar yadda aka shirya.”

Ya kuma bukaci al’umma kasashen duniya su kaucewa dukkan ayyukan da zai iya haifar da barazana ga wannan rana ta hanyar yin wasu furuce-furice a kafafen sadarwa na zaman ida za su iya harfar da tashin hankali.

Sufeton
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

An Nemi Sabuwar Gwamnatin Kano Ta Kawo Dauki Kan Hauhawar Farashi

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.