• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Magana

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Magana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fari, da ambaliyar ruwa, kwararar hamada, yanayi na sanyi da zafi da suka wuce kima da makamantansu, na daga cikin matsalolin da sauyin yanayi ke haddasawa, wadanda kuma ke ci gaba da addabar bil-adama. Bayanai na nuna cewa, kasashen dake yankin kahon Afirka na daga cikin wadanda ke fama da wannan matsala.

Sakamakon matsalar fari da yankin kahon Afirka ke fuskanta, ya sa asusun tallafawa kananan yara na MDD ko UNICEF a takaice, ya kaddamar da asusun gaggawa, inda yake neman taimakon dalar Amurka biliyan daya, domin tallafawa yaran dake rayuwa a sassan yankin kahon Afirka a shekarar 2023 dake tafe.

  • Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

UNICEF ya ce, ya sake nazartar kudaden tallafin gaggawa na jin kai da ake bukata, domin kare rayuwar yara dake kasashen Habasha, da Kenya da Somaliya, inda adadin kudaden da ake bukata domin gudanar da ayyuka ya sauya, daga dala miliyan 879 a watan Satumba zuwa dala biliyan daya a shekara mai zuwa. Babbar magana wai Dan-sanda ya ga gawar soja.

Wannan na zuwa ne, bayan asusun da aka kaddamar a taron sauyin yanayi na kasar Masar, duk da nufin magance illar da wannan matsala ta sauyin yanayi ke haifarwa duniyar bil-Adama da abubuwan dake rayuwa a cikinta.

Bayanai na nuna cewa, yaran dake yankin kahon Afirka na fuskantar mawuyacin hali na rayuwa, sakamakon mummunan fari da aka jima ba a ga irin sa ba a tarihin kasashen 3, baya ga tashe-tashen hankula dake ci gaba da addabar arewacin Habasha. Don haka, taimakawa wannan rukuni na al’umma dake zama manyan gobe, zai taimaka ga ci gaban al’ummar yankin ne baki daya.

Labarai Masu Nasaba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Masharhanta na cewa, mummunan tasirin sauyin yanayi na barazana ga rayukan yara, abin da ya sanya asusun mayar da hankali, ga dabarun jurewa da iya rayuwa tare da tasirin sauyin yanayi, a matsayin muhimman bangarorin tallafin jin kai da yake aiwatarwa. Kuma hakan zai taimaka matuka, wajen kaiwa ga yaran dake rayuwa cikin yanayin tashe-tashen hankula, tare da ba da damar taimaka musu, da al’ummun su shiryawa abubuwan daka iya aukuwa a nan gaba. Rigakafi aka ce ya fi magani. Fata dai shi ne, kudaden da za a tara za su kai ga wadanda aka yi dominsu. Domin ka da a fake da guzuma ana harbin karsana. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qatar 2022: Za A Mayar Da Dakin Otal Din Da Messi Ya Zauna Wajen Tarihi

Next Post

Rashin Amincewa Da Daidaita Tsarin Rigakafi Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Na Sin Ya Saba Gaskiya

Related

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

2 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

2 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

3 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

4 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

5 hours ago
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

6 hours ago
Next Post
Rashin Amincewa Da Daidaita Tsarin Rigakafi Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Na Sin Ya Saba Gaskiya

Rashin Amincewa Da Daidaita Tsarin Rigakafi Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Na Sin Ya Saba Gaskiya

LABARAI MASU NASABA

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.