• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasa Cristiano Ronaldo ya bayyana cewa daga yanzu babu sauran adawa tsakaninsa da babban abokin hamayyarsa a fagen kwallon kafa, wato Lionel Messi, inda a cewarsa sun sauya tarihin kwallon kafar duniya. Ronaldo da Messi, ‘yan wasa biyu ne da ake yi wa lakabi da, ‘yan wasan da suka fi shahara a tarihi, wato ‘Gaot’ – sun sha fuskantar juna a lokacin da suke buga gasar La Liga a kungiyoyin Real Madrid da Barcelona.

Dan wasa Ronaldo ya ce dukkannin su ana girmama su a duniya, wannan shi ne babban abu mafi muhimmanci saboda haka lokaci ya yi da adawa a tsakanin su za ta zo karshe.
Ronaldo wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar – a bana baya cikin mutanen da ke takarar kyautar karon farko tun shekara ta 2003, yayin da Messi zai iya lashe kyautar karo takwas a tarihi.

  • Ronaldo, Neymar Da Benzema Na Fatan Lashe Gasar Zakarun Asia

“Ya kafa tarihi, ni ma na kafa nawa, ya yi abin da ya dace, daga abin da na gani,” in ji Ronaldo mai shekara 38 a duniya wanda a yanzu yake buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya.

Dan kasar Portugal din ya ci gaba da cewa “bai kamata wadanda ke son Ronaldo, su ki Messi ba kuma a yanzu adawa ta kare, sun shafe shekara 15 suna jan zare a harkar kwallon kafa, don haka yanzu sun wuce abokai, sun zaman kwararrun abokan sana’a, kuma suna girmama junansu”.

‘Yan wasan sun cimma nasarori masu yawa a fagen wasan kwallon kafa, inda suka lashe kyaututtuka masu dimbin yawa a harkar kwallon kafa a matakin kungiyoyi da kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

Ronaldo shi ne dan wasan da ya fi kowa zira kwallaye a Real Madrid inda ya ci 451 a wasa 438 da ya yi wa kungiyar, tare da cin kofuna 16 ciki har da Kofin Champions Leagues hudu da na La Liga biyu da na Copa del Rey biyu a tsowan shekara tara da ya yi a Real Madrid.

Shi kuwa Messi – wanda a yanzu ke wasa a kungiyar Inter Miami ta Amurka – ya kasance dan wasan da ya fi ci wa Barcelona kwallaye inda ya ci 674 a wasa 781 da ya buga wa kungiyar.

Messi – mai shekara 36 ya lashe kofuna 35 a Barcelona, ciki har da kofin La Liga 10 da kofin Champions League hudu da Copa del Rey bakwai a iya zaman da ya yi a kungiyar ta kasar Spaniya.

A matakin kasa kuwa Messi ya taimaka wa Argentina lashe Kofin Duniya da aka buga a Katar a 2022, sannan ya dauki kofin Copa America, yayin da shi kuma Ronaldo ya taimaka wa Portugal daukar kofin nahiyar Turai da kofin ‘Nations League’.

‘Yan wasan sun fuskanci juna a fili sau 36, haduwarsu ta karshe shi ne a watan Janairu a lokacin da kungiyar Messi ta PSG ta doke ta Al-Nassr da ci 5-4 a wasan sada zumunta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MessiSaudi pro leagueUEFA Champions League
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Daɗe Ana Yi Sai Gaskiya

Next Post

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Related

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

17 hours ago
Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Wasanni

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

1 day ago
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

2 days ago
‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana
Wasanni

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

2 days ago
Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United
Wasanni

Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

3 days ago
Tottenham Ta Ɗauki Xavi Simons Daga RB Leipzig
Wasanni

Tottenham Ta Ɗauki Xavi Simons Daga RB Leipzig

4 days ago
Next Post
Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.