• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasa Cristiano Ronaldo ya bayyana cewa daga yanzu babu sauran adawa tsakaninsa da babban abokin hamayyarsa a fagen kwallon kafa, wato Lionel Messi, inda a cewarsa sun sauya tarihin kwallon kafar duniya. Ronaldo da Messi, ‘yan wasa biyu ne da ake yi wa lakabi da, ‘yan wasan da suka fi shahara a tarihi, wato ‘Gaot’ – sun sha fuskantar juna a lokacin da suke buga gasar La Liga a kungiyoyin Real Madrid da Barcelona.

Dan wasa Ronaldo ya ce dukkannin su ana girmama su a duniya, wannan shi ne babban abu mafi muhimmanci saboda haka lokaci ya yi da adawa a tsakanin su za ta zo karshe.
Ronaldo wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar – a bana baya cikin mutanen da ke takarar kyautar karon farko tun shekara ta 2003, yayin da Messi zai iya lashe kyautar karo takwas a tarihi.

  • Ronaldo, Neymar Da Benzema Na Fatan Lashe Gasar Zakarun Asia

“Ya kafa tarihi, ni ma na kafa nawa, ya yi abin da ya dace, daga abin da na gani,” in ji Ronaldo mai shekara 38 a duniya wanda a yanzu yake buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya.

Dan kasar Portugal din ya ci gaba da cewa “bai kamata wadanda ke son Ronaldo, su ki Messi ba kuma a yanzu adawa ta kare, sun shafe shekara 15 suna jan zare a harkar kwallon kafa, don haka yanzu sun wuce abokai, sun zaman kwararrun abokan sana’a, kuma suna girmama junansu”.

‘Yan wasan sun cimma nasarori masu yawa a fagen wasan kwallon kafa, inda suka lashe kyaututtuka masu dimbin yawa a harkar kwallon kafa a matakin kungiyoyi da kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Ronaldo shi ne dan wasan da ya fi kowa zira kwallaye a Real Madrid inda ya ci 451 a wasa 438 da ya yi wa kungiyar, tare da cin kofuna 16 ciki har da Kofin Champions Leagues hudu da na La Liga biyu da na Copa del Rey biyu a tsowan shekara tara da ya yi a Real Madrid.

Shi kuwa Messi – wanda a yanzu ke wasa a kungiyar Inter Miami ta Amurka – ya kasance dan wasan da ya fi ci wa Barcelona kwallaye inda ya ci 674 a wasa 781 da ya buga wa kungiyar.

Messi – mai shekara 36 ya lashe kofuna 35 a Barcelona, ciki har da kofin La Liga 10 da kofin Champions League hudu da Copa del Rey bakwai a iya zaman da ya yi a kungiyar ta kasar Spaniya.

A matakin kasa kuwa Messi ya taimaka wa Argentina lashe Kofin Duniya da aka buga a Katar a 2022, sannan ya dauki kofin Copa America, yayin da shi kuma Ronaldo ya taimaka wa Portugal daukar kofin nahiyar Turai da kofin ‘Nations League’.

‘Yan wasan sun fuskanci juna a fili sau 36, haduwarsu ta karshe shi ne a watan Janairu a lokacin da kungiyar Messi ta PSG ta doke ta Al-Nassr da ci 5-4 a wasan sada zumunta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MessiSaudi pro leagueUEFA Champions League
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Daɗe Ana Yi Sai Gaskiya

Next Post

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

4 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

4 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

7 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

1 week ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.