• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasa Cristiano Ronaldo ya bayyana cewa daga yanzu babu sauran adawa tsakaninsa da babban abokin hamayyarsa a fagen kwallon kafa, wato Lionel Messi, inda a cewarsa sun sauya tarihin kwallon kafar duniya. Ronaldo da Messi, ‘yan wasa biyu ne da ake yi wa lakabi da, ‘yan wasan da suka fi shahara a tarihi, wato ‘Gaot’ – sun sha fuskantar juna a lokacin da suke buga gasar La Liga a kungiyoyin Real Madrid da Barcelona.

Dan wasa Ronaldo ya ce dukkannin su ana girmama su a duniya, wannan shi ne babban abu mafi muhimmanci saboda haka lokaci ya yi da adawa a tsakanin su za ta zo karshe.
Ronaldo wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar – a bana baya cikin mutanen da ke takarar kyautar karon farko tun shekara ta 2003, yayin da Messi zai iya lashe kyautar karo takwas a tarihi.

  • Ronaldo, Neymar Da Benzema Na Fatan Lashe Gasar Zakarun Asia

“Ya kafa tarihi, ni ma na kafa nawa, ya yi abin da ya dace, daga abin da na gani,” in ji Ronaldo mai shekara 38 a duniya wanda a yanzu yake buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya.

Dan kasar Portugal din ya ci gaba da cewa “bai kamata wadanda ke son Ronaldo, su ki Messi ba kuma a yanzu adawa ta kare, sun shafe shekara 15 suna jan zare a harkar kwallon kafa, don haka yanzu sun wuce abokai, sun zaman kwararrun abokan sana’a, kuma suna girmama junansu”.

‘Yan wasan sun cimma nasarori masu yawa a fagen wasan kwallon kafa, inda suka lashe kyaututtuka masu dimbin yawa a harkar kwallon kafa a matakin kungiyoyi da kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Ronaldo shi ne dan wasan da ya fi kowa zira kwallaye a Real Madrid inda ya ci 451 a wasa 438 da ya yi wa kungiyar, tare da cin kofuna 16 ciki har da Kofin Champions Leagues hudu da na La Liga biyu da na Copa del Rey biyu a tsowan shekara tara da ya yi a Real Madrid.

Shi kuwa Messi – wanda a yanzu ke wasa a kungiyar Inter Miami ta Amurka – ya kasance dan wasan da ya fi ci wa Barcelona kwallaye inda ya ci 674 a wasa 781 da ya buga wa kungiyar.

Messi – mai shekara 36 ya lashe kofuna 35 a Barcelona, ciki har da kofin La Liga 10 da kofin Champions League hudu da Copa del Rey bakwai a iya zaman da ya yi a kungiyar ta kasar Spaniya.

A matakin kasa kuwa Messi ya taimaka wa Argentina lashe Kofin Duniya da aka buga a Katar a 2022, sannan ya dauki kofin Copa America, yayin da shi kuma Ronaldo ya taimaka wa Portugal daukar kofin nahiyar Turai da kofin ‘Nations League’.

‘Yan wasan sun fuskanci juna a fili sau 36, haduwarsu ta karshe shi ne a watan Janairu a lokacin da kungiyar Messi ta PSG ta doke ta Al-Nassr da ci 5-4 a wasan sada zumunta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MessiSaudi pro leagueUEFA Champions League
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Daɗe Ana Yi Sai Gaskiya

Next Post

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Related

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

17 hours ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

2 days ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

3 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

4 days ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

4 days ago
Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa
Wasanni

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

4 days ago
Next Post
Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.