ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

by CMG Hausa
3 years ago
Kasashe masu tasowa

“Yanzu haka kasashe masu tasowa na samun ci gaba cikin sauri, inda suke samar da karin tasiri a duniya. Wannan wani yanayi ne mai yakini wanda ba za a iya sauya shi ba.” Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fadi haka a kwanan baya, yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Zambia Hakainde Hichilema. Wannan zance ya nuna ra’ayinsa game da sauyawar yanayin da ake samu kan tsare-tsaren duniya.

Hakika ana iya ganin yadda kasashe masu tasowa suke samun karin karfi, bisa tantance wasu abubuwan da suka abku a kwanan baya. Misali, an shigar da kungiyar kasashen Afirka ta AU cikin rukunin kasashe masu karfin tattalin arziki ta G20, kana an yarda da sanya karin wasu mambobi 6 cikin tsarin hadin gwiwa na kasashen BRICS (Brazil, Rasha, India, Sin, da Afirka ta Kudu).

  • Birnin Shanghai Ya Karbi Bakuncin Bikin Yawon Bude Ido Na 34 Domin Bunkasa Fannin Yawon Shakatawa

Ban da haka, an gabatar da sabbin matakai na taimakawa kasashen Afirka cimma burinsu na dunkule tattalin arzikinsu waje guda, da zamanantar da kasashensu, wajen wani taron musayar ra’ayi na shugabannin kasashen Afirka da Sin.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, a wajen taron shugabannin rukunin kasashe 77 (wata kungiyar hadin gwiwar kasashe masu tasowa) da kasar Sin, da aka kammala shi jiya Lahadi a kasar Cuba, an gabatar da sanarwar karfafa hadin kan kasashe masu tasowa, da niyyarsu ta kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa. Duk wadannan abubuwa sun nuna karuwar karfin kasashe masu tasowa.

Sai dai babu shakka, wannan yanayi mai yakini da kasashe masu tasowa suke ciki zai janyo hassada, da kokarin hana ruwa gudu daga wasu kasashe masu sukuni. Hakan ya sa ake yin kokarin bayyana ra’ayin rashin amincewa da kashin dankali da ake yi a duniya, a wajen taron rukunin kasashe 77 da kasar Sin. Inda dimbin shugabanni, da manyan jami’ai na kasashe masu tasowa suka yi kira da a kawo karshen wani “ tsarin kasa da kasa mai cike da ayyukan kwatar dukiyoyi”, tare da bukatar dukkan kasashe masu tasowa da su gyara ka’idojin da ake bi yayin da ake tafiyar da harkokin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Ban da haka, sanarwar Havana da aka gabatar wajen taron ta nuna yadda ake kin yarda da tsare-tsaren duniya maras adalci, inda aka yi Allah wadai da matakan tilastawa sauran kasashe yin wani abu, da sanyawa kasashe masu tasowa takunkumi, da hana su samun damar raya fasahohi na zamani, da dai sauransu.

Dalilin da ya sa kasashe masu tasowa ke kin amincewa da tsoffin tsare-tsaren kasa da kasa, shi ne suna neman maye gurbinsu da wani sabon tsari mai adalci, wanda zai ba su damar kare moriyar kai, da neman samun ci gaban tattalin arziki ba tare da wata matsalar da aka haifar musu ba. Sai dai ta yaya za a iya cimma wannan buri? A wajen taron rukunin kasashe 77 da kasar Sin na wannan karo, bangaren kasar Sin ya ba da shawara cewa, da farko, a yi kokarin dogaro da kai, da magance yin fito-na-fito da sauran kasashe, da neman daidaita sabanin ra’ayi ta hanyar sulhu. Na biyu shi ne, a yi kokarin tabbatar da adalci yayin da ake kula da harkokin kasa da kasa, da kare moriyar kasashe masu tasowa, da sanya su zama masu fada a ji a duniya. Kana abu na uku shi ne, a yi karin hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, don tabbatar da ci gaban tattalin arzikinsu, da daga matsayinsu a duniya ta fuskar raya sabbin fasahohi da sana’o’i.

Hakika a wannan zamanin da muke ciki, karfin kasashen yamma a fannin tattalin arziki da siyasa na raguwa, don haka sun kara nuna halayyarsu ta son kai, da rashin hankali. Wannan ya sa kasashe masu tasowa ke bukatar yin hadin gwiwa a tsakaninsu, don magance a ci zarafinsu. Daga baya wannan yanayin da ake ciki ya sa muke ganin dimbin kasashe masu tasowa ke kokarin rufa wa juna baya a sassa daban daban, da fito da murya iri daya. Ta la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke kunsar mafi yawan kasashe da al’umma a duniyarmu, hadin gwiwar su zai tabbatar da hauhawar matsayinsu a duniya a kai a kai. (Bello Wang)

Kasashe masu tasowa
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Mao

Amurka Ba Ta Da Ikon Sukar Sin Game Da Yaduwar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.