• Leadership Hausa
Friday, December 8, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

by CMG Hausa
3 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Yanzu haka kasashe masu tasowa na samun ci gaba cikin sauri, inda suke samar da karin tasiri a duniya. Wannan wani yanayi ne mai yakini wanda ba za a iya sauya shi ba.” Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fadi haka a kwanan baya, yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Zambia Hakainde Hichilema. Wannan zance ya nuna ra’ayinsa game da sauyawar yanayin da ake samu kan tsare-tsaren duniya.

Hakika ana iya ganin yadda kasashe masu tasowa suke samun karin karfi, bisa tantance wasu abubuwan da suka abku a kwanan baya. Misali, an shigar da kungiyar kasashen Afirka ta AU cikin rukunin kasashe masu karfin tattalin arziki ta G20, kana an yarda da sanya karin wasu mambobi 6 cikin tsarin hadin gwiwa na kasashen BRICS (Brazil, Rasha, India, Sin, da Afirka ta Kudu).

  • Birnin Shanghai Ya Karbi Bakuncin Bikin Yawon Bude Ido Na 34 Domin Bunkasa Fannin Yawon Shakatawa

Ban da haka, an gabatar da sabbin matakai na taimakawa kasashen Afirka cimma burinsu na dunkule tattalin arzikinsu waje guda, da zamanantar da kasashensu, wajen wani taron musayar ra’ayi na shugabannin kasashen Afirka da Sin.

Haka kuma, a wajen taron shugabannin rukunin kasashe 77 (wata kungiyar hadin gwiwar kasashe masu tasowa) da kasar Sin, da aka kammala shi jiya Lahadi a kasar Cuba, an gabatar da sanarwar karfafa hadin kan kasashe masu tasowa, da niyyarsu ta kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa. Duk wadannan abubuwa sun nuna karuwar karfin kasashe masu tasowa.

Sai dai babu shakka, wannan yanayi mai yakini da kasashe masu tasowa suke ciki zai janyo hassada, da kokarin hana ruwa gudu daga wasu kasashe masu sukuni. Hakan ya sa ake yin kokarin bayyana ra’ayin rashin amincewa da kashin dankali da ake yi a duniya, a wajen taron rukunin kasashe 77 da kasar Sin. Inda dimbin shugabanni, da manyan jami’ai na kasashe masu tasowa suka yi kira da a kawo karshen wani “ tsarin kasa da kasa mai cike da ayyukan kwatar dukiyoyi”, tare da bukatar dukkan kasashe masu tasowa da su gyara ka’idojin da ake bi yayin da ake tafiyar da harkokin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Ban da haka, sanarwar Havana da aka gabatar wajen taron ta nuna yadda ake kin yarda da tsare-tsaren duniya maras adalci, inda aka yi Allah wadai da matakan tilastawa sauran kasashe yin wani abu, da sanyawa kasashe masu tasowa takunkumi, da hana su samun damar raya fasahohi na zamani, da dai sauransu.

Dalilin da ya sa kasashe masu tasowa ke kin amincewa da tsoffin tsare-tsaren kasa da kasa, shi ne suna neman maye gurbinsu da wani sabon tsari mai adalci, wanda zai ba su damar kare moriyar kai, da neman samun ci gaban tattalin arziki ba tare da wata matsalar da aka haifar musu ba. Sai dai ta yaya za a iya cimma wannan buri? A wajen taron rukunin kasashe 77 da kasar Sin na wannan karo, bangaren kasar Sin ya ba da shawara cewa, da farko, a yi kokarin dogaro da kai, da magance yin fito-na-fito da sauran kasashe, da neman daidaita sabanin ra’ayi ta hanyar sulhu. Na biyu shi ne, a yi kokarin tabbatar da adalci yayin da ake kula da harkokin kasa da kasa, da kare moriyar kasashe masu tasowa, da sanya su zama masu fada a ji a duniya. Kana abu na uku shi ne, a yi karin hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, don tabbatar da ci gaban tattalin arzikinsu, da daga matsayinsu a duniya ta fuskar raya sabbin fasahohi da sana’o’i.

Hakika a wannan zamanin da muke ciki, karfin kasashen yamma a fannin tattalin arziki da siyasa na raguwa, don haka sun kara nuna halayyarsu ta son kai, da rashin hankali. Wannan ya sa kasashe masu tasowa ke bukatar yin hadin gwiwa a tsakaninsu, don magance a ci zarafinsu. Daga baya wannan yanayin da ake ciki ya sa muke ganin dimbin kasashe masu tasowa ke kokarin rufa wa juna baya a sassa daban daban, da fito da murya iri daya. Ta la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke kunsar mafi yawan kasashe da al’umma a duniyarmu, hadin gwiwar su zai tabbatar da hauhawar matsayinsu a duniya a kai a kai. (Bello Wang)

Tags: AfirkaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

Next Post

Amurka Ba Ta Da Ikon Sukar Sin Game Da Yaduwar Miyagun Kwayoyi

Related

Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

4 hours ago
Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

4 hours ago
Sinawa: Mutane Masu Kwazo Da Girmama Baki Da Ke Kallon Alkiblar Kawo Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Sinawa: Mutane Masu Kwazo Da Girmama Baki Da Ke Kallon Alkiblar Kawo Ci Gaba

4 hours ago
Sin: Matakan Kuntatawa Na Kasar Amurka Kan Kasar Sin Ba Zai Hana Bunkasuwar Sin Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Matakan Kuntatawa Na Kasar Amurka Kan Kasar Sin Ba Zai Hana Bunkasuwar Sin Ba

4 hours ago
Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

6 hours ago
Shugabancin JKS Ya Gudanar Da Taro Game Da Ayyukan Raya Tattalin Arzikin Kasa Na 2024
Daga Birnin Sin

Shugabancin JKS Ya Gudanar Da Taro Game Da Ayyukan Raya Tattalin Arzikin Kasa Na 2024

8 hours ago
Next Post
Mao

Amurka Ba Ta Da Ikon Sukar Sin Game Da Yaduwar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

oktoba

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

December 8, 2023
Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

December 8, 2023
Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

December 8, 2023
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

December 8, 2023
Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

December 8, 2023
Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

December 8, 2023
Sinawa: Mutane Masu Kwazo Da Girmama Baki Da Ke Kallon Alkiblar Kawo Ci Gaba

Sinawa: Mutane Masu Kwazo Da Girmama Baki Da Ke Kallon Alkiblar Kawo Ci Gaba

December 8, 2023
Sin: Matakan Kuntatawa Na Kasar Amurka Kan Kasar Sin Ba Zai Hana Bunkasuwar Sin Ba

Sin: Matakan Kuntatawa Na Kasar Amurka Kan Kasar Sin Ba Zai Hana Bunkasuwar Sin Ba

December 8, 2023
Gwamna Yusuf

Gwamnan Kano Zai Gana Da Shugaban ‘Yan Fansho Kan Batan Naira Biliyan 5

December 8, 2023
Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

December 8, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.