• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Maganar Janye Wa Ahmed Lawan Takara — Hon. Bashir Machina

by Sulaiman and Muhammad Maitela
3 years ago
in Siyasa
0
Bashir Machina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar majalisar dattawa na Yobe ta arewa karkashin jam’iyyar APC, Hon. Bashir Sheriff Machina ya bayyana cewa shi ne daliget suka zaba a matsayin dan takara a zaben fid da gwani na jam’iyyar APC a yankin arewacin Yobe, domin haka babu batun wani kuma ya zama dan takara.

Hon. Bashir Machina ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci dakin watsa shirye-shirye na Podcast na Kamfanin LEADERSHIP da ke Abuja.

  • Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan

Ya kara da cewa yana tabbatar wa jama’an da suka zabe shi a matsayin dan takarar da ma ‘yan Nijeriya cewa, zaben da aka gudanar yana nan daram kuma shi ne sahihin dan takara wanda jam’iyyar APC ta tsayar.

Ya dai musanta janye takararsa domin ya bai wa Sanata Ahmed Lawan, inda ya ce wannan labarin ba gaskiya ba ne. Ya ce babu wata magana irin wannan da ta taba faruwa tsakaninsa da Sanata Ahmed Lawan na ya janye masa takara.

Haka kuma ya bayyana cewa yana bukatar zama dan majalisar dattawa ne domin ya zamanantar da yanayin wakilci a matsayinsa na matashi duba da yadda Sanata Ahmed Lawan ya gudanar da tasa wakilcin na tsawon lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Sannan ya sha alwashin gudanar da wakilcin da ya dace da zai kawo sauki cikin karamin lokaci, domin ya tabbata yana da kwarewa da zai iya karawa daga inda Ahmed Lawan ya tsaya.

A cewarsa, shi dan siyasa ne mai biyayya ga uwar jam’iyya wanda ya kwashe tsawan shekaru 30 a cikinta, amma a cewarsa ita jam’iyya tana da ka’idoji da kuma dokoki wanda take tsayuwa a kansu, sannan da wannan dokokin ne ta bi wajen gudanar da zaben fid da gwani har ya samu nasara, saboda haka jam’iyya APC ba za ta taba cewa ya zo a yi wata magana da ta saba wa ko’idojinta ba.

Ya ce Ahmed Lawan ya bi ka’idoji ne har ya tsaya takarar shugaban kasa a karkashiun jam’iyyar APC, kuma shi ma wannan ka’idojin ne ya bi har aka zabe shi a matsayin dan takarar dan majalisan dattawa na yankin arewacin Yobe.

Hon. Bashir Machina ya ce jam’iyyar APC ta shaffida adalci wajen fitar da dan takarar shugaban kasa wanda har Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara.
Ya ce idan ya samu damar zama dan majalisar dattawa na yankin arewacin Yobe zai yi kokarin hada kan jama’a wajen samar da tsaro a cikin jiharsa. Ya dai cewa matsalar tsaro ba za a iya magance shi ba har sai an hada hannu da karfe a tsakanin jami’an tsaro da kuma al’umma.

A cewarsa, yana da gwarin gwiwar lashe zabe a 2023, domin jama’a ne suka zabe shi a matsayin dan takarar sanata, sannan kuma jam’iyyarsa tana da gagarumin rinjaye a Jihar Yobe wanda zai iya samun nasara.

Ya ce a matsayinsa na dan siyasa zai dunga bin ra’ayin jama’a ne kan duk wani tsari da ya shafi wakilcinsa.
Har ila yau, Al’ummar Bade da Jakusko sun goyi bayan Hon. Machina.

A lokacin da takkadama ke ci gaba da zafafa tsakanin shugaban majalisan dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan, da dan takarar Sanatan arewacin Yobe, Hon. Bashir Sharif Machina; biyo bayan kayen da Sanata Lawan ya sha a zaben fid da gwani na shugaban kasa da jam’iyyar APC ya gudanar a makon da ya gabata da kuma nasarar zaben fid da gwani da Machina ya samu a daya bangaren.

Wasu majiyoyi sun nuna cewa har yanzu Hon. Lawan yana hararar kujerar tare da bayyana bukatarsa ga Hon. Machina ya janye masa, bayan lashe zaben fid da gwani na takarar sanata na arewacin Yobe, al’amarin da ke ci gaba da daukar hankulan ‘yan Nijeriya.

A daidai wannan gabar, al’ummar kananan hukumomin Bade da Jakusko da ke Jihar Yobe sun fito kan tituna domin bayyana goyon bayansu ga takarar Hon. Machina, a tsakiyar wannan mako a garin Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade. Dubban jama’ar sun ziyarci fadar Sarkin Bade; Maimartaba Abubakar Umar Suleiman, domin mika gaisuwar girma tare da bayyana makasudin taron, wanda ya kunshi mata, matasa da masu ruwa da tsaki a siyasar yankin.

Da yake bayani ga manema labarai jim kadan da kammala taron, Barista Hamza Hashimu Karage, ya bayyana cewa, a matsayinsu na al’ummar masarautar Bade, sun yaba da hidimar da Sanata Ahmed Lawan ya yi wa kasa na kimanin shekaru 16 a zauren majalisar dattawan Nijeriya, inda har Allah ya kai shi zuwa shugaban majalisar, wanda hakan ba karamin abin alfahari bane ga al’ummar masarautar baki daya.

Bugu da kari kuma, ya ce “Muna alfahari da Sanata Ahmed Lawan bisa bajintar da yayi na takarar kujerar shugaban kasa a jam’iyyar APC a zaben fid da gwani da ya gabata tare da bayyana bakin cikin rashin nasarar da ya yi a zaben.”

Ya ce, Hon. Bashir Machina gogaggen dan siyasa ne wanda ya samu nasarar zaben fid da gwani a kujerar Sanatan Zone C, wanda bisa hakan ne suke bayyana cikakken goyon bayansu gare shi domin samun nasara a babban zabe mai zuwa na 2023.

Ya ce, “Muna kira ga dukan ‘ya’yan jam’iyyar APC ciki har da na PDP da ke arewacin Yobe su goyi bayan Hon. Machina don samun gagarumar nasara a zabe mai zuwa. Kuma ina kara ba ku tabbacin cewa mu da matasa tare da dattawanmu a wannan yankin za mu hada hannu waje daya domin ganin Hon. Bashir Machina ya yi nasara.”

A nasa bangaren, tsohon shugaban karamar hukumar Jakusko, Hassan Kaku Lawan ya bayyana cewa, “Wannan taro ne na nuna goyon bayan al’ummar Bade da Jakusko ga dan takarar kujerar Sanatan Arewacin Yobe, Hon. Bashir Machina, wanda ya hada kowane bangaren jama’a, a matsayin yadda su ma al’ummar Machina da sauran kananan hukumomin wannan yankin suka mara wa namu Sanata a baya; Sanata Ahmed Lawan a shekarun da suka gabata.

“A hannu guda kuma, al’ummar wannan masarauta ta Bade suna bayyana cikakken goyon bayan su ga takarar Hon. Bashir Machina, bisa makamancin irin wannan goyon baya da suka samu daga masarautar Nguru da Machina a lokutan da Sanata Ahmed Lawan ya dauka yana rike da kujerar majalisar dattawan yankin, saboda haka muna goyon bayansa dari-bisa-dari.”

Shi kuwa tsohon mukaddashin sakataren tsohuwar jam’iyyar ANPP a Jihar Yobe, Mohammed D. Sa’idu (Gaskanta) ya tofa nasa albarkacin bakinsa da cewa, “Kamar yadda ka ce cin tuwon kishiya ramako, ko shakka babu haka zancen yake. Saboda kimanin shekaru 16 da suka gabata, ita ma masarautar Nguru ta rike kujerar Sanatan Arewacin Yobe, wanda an shirya wannan taron ne domin bayyana goyon bayan al’ummar Bade da Jakusko ga takarar Hon. Bashir Machina a matsayin rama hadin kai da goyon bayan da suka nuna mana a wadannan shekaru ga Sanata Ahmed Lawan.”

A nasa bayanin, shugaban taron kuma tsohon kwamishina a ma’aikatar wasanni da matasa ta Jihar Yobe, Mallam Saleh Kachalla ya bayyana makasudin taron da cewa, “A matsayinmu na al’ummar Bade da Jakusko; makasudin shirya wannan gangamin shi ne domin bayyana goyon bayanmu ga takarar kujerar Sanatan Arewacin Yobe wadda Hon. Bashir Sharif Machina zai yi, muna yi masa fatan alheri tare da samun goyon bayanmu a babban zabe mai zuwa a 2023.”

A hannu guda kuma, kwamitin yakin neman zaben Hon. Bashir Sharif Machina ya karyata bayanan da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani cewa Hon. Bashir Sharif Machina ya janye takararsa, wanda kwamitin ya bayyana wannan zance a matsayin maras tushe ballantana makama, tare da sake tabbatar wa jama’a cewa har yanzu dan takarar yana nan kan bakarsa na dan takarar Sanatan Arewacin Yobe a zaben 2023 mai zuwa.

A wata sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin, Alhaji Shehu Riga, ya bayyana cewa, “Babu wani lokaci a kowane yanayi da Hon. Machina ya taba sanya hannu ko bayani dangane da batun janyewa wani takarar da yake na kujerar Sanatan Arewacin Yobe. Saboda haka muna kira ga jama’a su yi watsi da wannan jita-jita marasa tushe ballantana makama.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum Biliyan 1 Ke Fama Da Tabin Hankali A Duniya — WHO

Next Post

Gidauniya Ta Ware Naira Miliyan 332.8 Don Tallafa Wa Karatun Yara A Katsina

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Gidauniya Ta Ware Naira Miliyan 332.8 Don Tallafa Wa Karatun Yara A Katsina

Gidauniya Ta Ware Naira Miliyan 332.8 Don Tallafa Wa Karatun Yara A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.