ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Maganar Janye Wa Ahmed Lawan Takara — Hon. Bashir Machina

by Sulaiman and Muhammad Maitela
4 years ago
Bashir Machina

Dan takarar majalisar dattawa na Yobe ta arewa karkashin jam’iyyar APC, Hon. Bashir Sheriff Machina ya bayyana cewa shi ne daliget suka zaba a matsayin dan takara a zaben fid da gwani na jam’iyyar APC a yankin arewacin Yobe, domin haka babu batun wani kuma ya zama dan takara.

Hon. Bashir Machina ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci dakin watsa shirye-shirye na Podcast na Kamfanin LEADERSHIP da ke Abuja.

  • Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan

Ya kara da cewa yana tabbatar wa jama’an da suka zabe shi a matsayin dan takarar da ma ‘yan Nijeriya cewa, zaben da aka gudanar yana nan daram kuma shi ne sahihin dan takara wanda jam’iyyar APC ta tsayar.

ADVERTISEMENT

Ya dai musanta janye takararsa domin ya bai wa Sanata Ahmed Lawan, inda ya ce wannan labarin ba gaskiya ba ne. Ya ce babu wata magana irin wannan da ta taba faruwa tsakaninsa da Sanata Ahmed Lawan na ya janye masa takara.

Haka kuma ya bayyana cewa yana bukatar zama dan majalisar dattawa ne domin ya zamanantar da yanayin wakilci a matsayinsa na matashi duba da yadda Sanata Ahmed Lawan ya gudanar da tasa wakilcin na tsawon lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Sannan ya sha alwashin gudanar da wakilcin da ya dace da zai kawo sauki cikin karamin lokaci, domin ya tabbata yana da kwarewa da zai iya karawa daga inda Ahmed Lawan ya tsaya.

A cewarsa, shi dan siyasa ne mai biyayya ga uwar jam’iyya wanda ya kwashe tsawan shekaru 30 a cikinta, amma a cewarsa ita jam’iyya tana da ka’idoji da kuma dokoki wanda take tsayuwa a kansu, sannan da wannan dokokin ne ta bi wajen gudanar da zaben fid da gwani har ya samu nasara, saboda haka jam’iyya APC ba za ta taba cewa ya zo a yi wata magana da ta saba wa ko’idojinta ba.

Ya ce Ahmed Lawan ya bi ka’idoji ne har ya tsaya takarar shugaban kasa a karkashiun jam’iyyar APC, kuma shi ma wannan ka’idojin ne ya bi har aka zabe shi a matsayin dan takarar dan majalisan dattawa na yankin arewacin Yobe.

Hon. Bashir Machina ya ce jam’iyyar APC ta shaffida adalci wajen fitar da dan takarar shugaban kasa wanda har Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara.
Ya ce idan ya samu damar zama dan majalisar dattawa na yankin arewacin Yobe zai yi kokarin hada kan jama’a wajen samar da tsaro a cikin jiharsa. Ya dai cewa matsalar tsaro ba za a iya magance shi ba har sai an hada hannu da karfe a tsakanin jami’an tsaro da kuma al’umma.

A cewarsa, yana da gwarin gwiwar lashe zabe a 2023, domin jama’a ne suka zabe shi a matsayin dan takarar sanata, sannan kuma jam’iyyarsa tana da gagarumin rinjaye a Jihar Yobe wanda zai iya samun nasara.

Ya ce a matsayinsa na dan siyasa zai dunga bin ra’ayin jama’a ne kan duk wani tsari da ya shafi wakilcinsa.
Har ila yau, Al’ummar Bade da Jakusko sun goyi bayan Hon. Machina.

A lokacin da takkadama ke ci gaba da zafafa tsakanin shugaban majalisan dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan, da dan takarar Sanatan arewacin Yobe, Hon. Bashir Sharif Machina; biyo bayan kayen da Sanata Lawan ya sha a zaben fid da gwani na shugaban kasa da jam’iyyar APC ya gudanar a makon da ya gabata da kuma nasarar zaben fid da gwani da Machina ya samu a daya bangaren.

Wasu majiyoyi sun nuna cewa har yanzu Hon. Lawan yana hararar kujerar tare da bayyana bukatarsa ga Hon. Machina ya janye masa, bayan lashe zaben fid da gwani na takarar sanata na arewacin Yobe, al’amarin da ke ci gaba da daukar hankulan ‘yan Nijeriya.

A daidai wannan gabar, al’ummar kananan hukumomin Bade da Jakusko da ke Jihar Yobe sun fito kan tituna domin bayyana goyon bayansu ga takarar Hon. Machina, a tsakiyar wannan mako a garin Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade. Dubban jama’ar sun ziyarci fadar Sarkin Bade; Maimartaba Abubakar Umar Suleiman, domin mika gaisuwar girma tare da bayyana makasudin taron, wanda ya kunshi mata, matasa da masu ruwa da tsaki a siyasar yankin.

Da yake bayani ga manema labarai jim kadan da kammala taron, Barista Hamza Hashimu Karage, ya bayyana cewa, a matsayinsu na al’ummar masarautar Bade, sun yaba da hidimar da Sanata Ahmed Lawan ya yi wa kasa na kimanin shekaru 16 a zauren majalisar dattawan Nijeriya, inda har Allah ya kai shi zuwa shugaban majalisar, wanda hakan ba karamin abin alfahari bane ga al’ummar masarautar baki daya.

Bugu da kari kuma, ya ce “Muna alfahari da Sanata Ahmed Lawan bisa bajintar da yayi na takarar kujerar shugaban kasa a jam’iyyar APC a zaben fid da gwani da ya gabata tare da bayyana bakin cikin rashin nasarar da ya yi a zaben.”

Ya ce, Hon. Bashir Machina gogaggen dan siyasa ne wanda ya samu nasarar zaben fid da gwani a kujerar Sanatan Zone C, wanda bisa hakan ne suke bayyana cikakken goyon bayansu gare shi domin samun nasara a babban zabe mai zuwa na 2023.

Ya ce, “Muna kira ga dukan ‘ya’yan jam’iyyar APC ciki har da na PDP da ke arewacin Yobe su goyi bayan Hon. Machina don samun gagarumar nasara a zabe mai zuwa. Kuma ina kara ba ku tabbacin cewa mu da matasa tare da dattawanmu a wannan yankin za mu hada hannu waje daya domin ganin Hon. Bashir Machina ya yi nasara.”

A nasa bangaren, tsohon shugaban karamar hukumar Jakusko, Hassan Kaku Lawan ya bayyana cewa, “Wannan taro ne na nuna goyon bayan al’ummar Bade da Jakusko ga dan takarar kujerar Sanatan Arewacin Yobe, Hon. Bashir Machina, wanda ya hada kowane bangaren jama’a, a matsayin yadda su ma al’ummar Machina da sauran kananan hukumomin wannan yankin suka mara wa namu Sanata a baya; Sanata Ahmed Lawan a shekarun da suka gabata.

“A hannu guda kuma, al’ummar wannan masarauta ta Bade suna bayyana cikakken goyon bayan su ga takarar Hon. Bashir Machina, bisa makamancin irin wannan goyon baya da suka samu daga masarautar Nguru da Machina a lokutan da Sanata Ahmed Lawan ya dauka yana rike da kujerar majalisar dattawan yankin, saboda haka muna goyon bayansa dari-bisa-dari.”

Shi kuwa tsohon mukaddashin sakataren tsohuwar jam’iyyar ANPP a Jihar Yobe, Mohammed D. Sa’idu (Gaskanta) ya tofa nasa albarkacin bakinsa da cewa, “Kamar yadda ka ce cin tuwon kishiya ramako, ko shakka babu haka zancen yake. Saboda kimanin shekaru 16 da suka gabata, ita ma masarautar Nguru ta rike kujerar Sanatan Arewacin Yobe, wanda an shirya wannan taron ne domin bayyana goyon bayan al’ummar Bade da Jakusko ga takarar Hon. Bashir Machina a matsayin rama hadin kai da goyon bayan da suka nuna mana a wadannan shekaru ga Sanata Ahmed Lawan.”

A nasa bayanin, shugaban taron kuma tsohon kwamishina a ma’aikatar wasanni da matasa ta Jihar Yobe, Mallam Saleh Kachalla ya bayyana makasudin taron da cewa, “A matsayinmu na al’ummar Bade da Jakusko; makasudin shirya wannan gangamin shi ne domin bayyana goyon bayanmu ga takarar kujerar Sanatan Arewacin Yobe wadda Hon. Bashir Sharif Machina zai yi, muna yi masa fatan alheri tare da samun goyon bayanmu a babban zabe mai zuwa a 2023.”

A hannu guda kuma, kwamitin yakin neman zaben Hon. Bashir Sharif Machina ya karyata bayanan da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani cewa Hon. Bashir Sharif Machina ya janye takararsa, wanda kwamitin ya bayyana wannan zance a matsayin maras tushe ballantana makama, tare da sake tabbatar wa jama’a cewa har yanzu dan takarar yana nan kan bakarsa na dan takarar Sanatan Arewacin Yobe a zaben 2023 mai zuwa.

A wata sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin, Alhaji Shehu Riga, ya bayyana cewa, “Babu wani lokaci a kowane yanayi da Hon. Machina ya taba sanya hannu ko bayani dangane da batun janyewa wani takarar da yake na kujerar Sanatan Arewacin Yobe. Saboda haka muna kira ga jama’a su yi watsi da wannan jita-jita marasa tushe ballantana makama.”

Bashir Machina
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Bashir Machina
Muhammad Maitela
+ posts Bio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
Gidauniya Ta Ware Naira Miliyan 332.8 Don Tallafa Wa Karatun Yara A Katsina

Gidauniya Ta Ware Naira Miliyan 332.8 Don Tallafa Wa Karatun Yara A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.