• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 hours ago
in Labarai
0
Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar din da ta gabata ne aka gudanar da taron gwamnonin jihohin Arewa a Kaduna, inda aka dauki matakai masu tsauri kan harkokin tsaro. A cikin wannan hirar, babban sakataren yada labarai na gwamnan jihar Kaduna, Malam Ibraheem Musa, ya bayyana cewa babu wani dan jarida da aka hana shi taron. ABDUL ya ruwaito haduwarsa da CPS na gwamna, inda ya tambaye shi shin ko me ya sa suka hana ‘yan jarida daukar labarai a taron kungiyar gwamnonin Arewa da aka yi ranar Asabar a gidan gwamnati Kaduna?

 

Me ya sa kuka hana ‘yan jarida yada labarai a taron kungiyar gwamnonin Arewa da aka yi ranar Asabar a gidan gwamnati Kaduna?

An dauki rahotannin taron yadda ya kamata; Tun daga bude taron har zuwa karshensa, yayin da shugaban kungiyar kuma gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammad Inuwa Yahaya ya karanta sanarwar. To, idan an hana ’yan jarida shiga taron, kamar yadda kuke fada, yaya aka yi aka samu labarin a kafofin yada labarai?

  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

An ruwaito cewa kun hana ‘yan jarida shiga wurin taron…

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

Sai ya ce “Na riga na amsa wannan tambayar amma har yanzu kana sake maimaita ta. Idan dai za a iya tunawa, ‘yan jarida 43 mazauna Kaduna ne suka halarci taron, ciki har da wasu ‘yan jarida daga wasu jihohin da suka raka gwamnonin nasu. Don haka, ba daidai ba ne a ce na hana ‘yan jarida shiga taron gwamnonin Arewa.

Duk jaridun kasar nan sun je a wurin. Duk gidajen rediyo da talbijin na Kaduna suna wurin. Duk wakilan manyan gidajen Talabijin da Rediyo da ke wajen Kaduna su ma suna nan. Kada ka dauki maganata a wani bangare daban, je ka bincika. Duk wadannan labarai ne irin na teburin mai shayi.

Ni kuma ban sani ba. Abin da na sani shi ne, idan kai dan jarida ne da ke Kaduna kuma ba ka cikin ’yan jarida 43 da aka gayyata ko kungiyoyin yada labarai, to akwai bukatar ka bincika shin ka cancanci a kira ka da dan jarida ko a’a. Akwai bambanci tsakanin ‘yan jarida da masu rubutun ra’ayin a Intanet. Kuma a cikin ‘yan jarida, akwai flotsam da jetsam da ake kira Press Center Press Corps, PCPC a takaice.

 

Menene asalin abin da ya faru a ranar Asabar da ya zama wasu dandali na intanet na kira a tsige ka a matsayin babban sakataren yada labarai?

Da farko ina yi wa Gwamnatin Jihar Kaduna hidima bisa yardar Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani. Zai iya cire ni ba tare da wani ya tambaye shi ya yi haka ba. Haka nan zai iya cire ni ba tare da dalili ba. Bayan na fadi haka, bari in amsa tambayarka.

A taron Gwamnonin Arewa kafin na karshe, sama da ‘yan jarida 100 ne suka halarci taron! Hakan ya zarce adadin bakin da dukkan ma’aikatan da gidan gwamnatin Kaduna suka gayyata. Mafi munin abin da ya faru, shi ne yadda wasunsu ba sa gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, sun koma zawarcin manyan mutane suna yin abin da shi ne ra’ayinsu.

Bayan taron, wasu ’yan uwana Sakatarorin Yada Labarai ko SA Media, sun koka, a madadin shugabanninsu. Don haka, a wannan karon, na dauki matakin daidaita lamarin lambar ta hanyar rubuta sunaye da kungiyoyin yada labarai na duk masu aiko da rahotanni da ’yan jarida na gida a cikin gidajen jaridu da na lantarki.

Jerin sunayen ya kai 43. Don haka, na aika da jerin sunayen ga Babban Jami’in Tsaron mu wanda ya aika da shi zuwa bakin kofar shiga fadar gwamnati wato ‘Gate’. Sai na bi diddigin wadanda na san mun gayyata. Don haka, idan ba sunanka a cikin wannan takarda kuma ba ka sami takardar gayyata ba, ba za a ba ka izinin shiga Gidan Gwamnati kai tsaye ba.

Kai duk da jerin sunayen mutane 43, sai da mkua samu matsala wajen shigar da su duka zauren majalisar inda gwamnoni da sarakunan gargajiya ke taro. An yi ta gwabza fada a kofar shiga zauren majalisar. Don haka, za ku iya tunanin idan ma an ce an gayyaci ‘yan jarida 100 ko fiye da hakan!

 

An zarge ku da cewa ba kowa kuka dauka ba, me ya sa yin hakan ya zama da wuya?

Yin hakan ba kawai wahala ba ne amma ba zai yiwu a dauki kowa da kowa ba. Na samu labarin cewa akwai ‘yan jarida kusan 400 a Kaduna, ta yaya zan iya daukar su duka?

Don Allah a gaya min, ku taimake ni. Yawan ’yan jarida, idan adadin ya yi daidai wannan ba matsala, amma ba zan iya daukar duk ‘yan jarida daga dukkan kafofiin yada labarai ba.

Ba za ka iya rubuta dandalin jaridun da suke a Online ba, ku tattara labarai daga wasu ku sake bugawa kuma kuna tsammanin zan dauke ku. Kuna iya daukar labarin ku watsa don kanku, za mu iya ba da labari idan bukatar hakan ta taso, zan iya ba da taimako. Amma ba zan iya daukar mutumin da ba zai iya rubuta labari ba, kawai don ya zo ya nuna min katin shaidar da shi ya yi domin kashin kansa.

NUJ tana da ayyuka da yawa da za ta yi wajen tsaftace sana’ar. Wasu daga cikin labaran da aka buga na cike da kura-kurai na nahawu da ya kamata a ce dan jarida ya san su. Wani abin damuwa shi ne wasu daga cikinsu sun shafe kusan shekaru 30 a aikin jarida, amma duk da haka, ba su da gogewa a aikin nasu. Abin takaici, sauran kwararru a harkar suna karanta labaran.

Amma kuma dole ne in yaba wa shugaban NUJ na kasa, Alhassan Yahya, da ya shiga lamarin, domin jin abin da ke faruwa, bayan jin labarin cewa wai na hana shiga, nan take ya kira ni kuma na yi masa bayanin abin da ya faru, na kuma bukaci ya kira wakilin kowace jarida ta kasa don jin ko akwai wanda aka hana shi yada labarin.

Na kuma mika jerin sunayen ‘yan jaridar da aka gayyata a gare shi. Saboda dattaku ya roki cewa mu yi kokarin ganin mun sasanta lamarin cikin lumana.

 

Ta yaya za ku warware wannan batu?

Babu abin da za a daidaita a nan. Idan da suna aiki da kafofin yada labarai masu inganci, da na kai karar kafofinsu ga kotu, ko kuma na kai kararsu ga NUJ ko Majalisar ‘yan Jarida ta Nijeriya. Amma kamar yadda na fada a baya. Sai dai kuma zan tuntubi lauyoyina domin su kai su kara domin an yi min kazafi a matsayina na Malam Ibraheem Musa.

‘Yancin fadin albarkacin baki ba lasisin bata suna bane. Mutane da yawa masu mutunci da manyan abokan aiki sun zo min suna fada min cewa in yi watsi da abin da aka rubuta a kaina domin duk wanda ya yi mu’amala da ni zai iya tabbatar da amincina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaJaridaKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

Next Post

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

Related

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta
Labarai

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

29 minutes ago
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe
Labarai

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

2 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

3 hours ago
Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya
Labarai

Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

6 hours ago
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

15 hours ago
Next Post
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

May 17, 2025
Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

Me Ya Sa Manchester United Ta Fi Yin Kokari A Europa League?

May 17, 2025
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

May 17, 2025
Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

May 17, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

May 17, 2025
Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya

May 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

May 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

May 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.