• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa kafin a fara aiwatar da duk wani irin aiki, dole ne a tantance ko ya dace ko bai dace ba, musamman ma game da muhimman ayyukan da ke shafar rayuka da lafiyar al’umma irinsu zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku.

  • Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Duk da haka, daga cikin dukkanin shirye-shirye da take iya zaba na sarrafa ruwan dagwalon, gwamnatin Japan ta zabi shirin zubar da ruwan cikin teku, saboda tsimin kudi da kuma rashin haifar da barazanar gurbacewar muhalli ga ita kanta, duk da hasarar da hakan ya haifarwa sauran kasashen duniya.

Idan ba a manta ba, a ranar 11 ga watan Maris na shekarar 2011, an yi girgizar kasa mai karfin maki 9 a tekun da ke arewa maso gabashin kasar ta Japan, girgizar da ta lalata tashar nukiliya ta Fukushima, har ma ta haddasa yoyon dimbin sinadaran nukiliya daga tashar. Ya zuwa shekarar 2021 kuma, gwamnatin Japan ta sanar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku bisa dalilinta na yadda ruwan ya kai iyakar da take iya adanawa, matakin da nan da nan ya jawo suka daga gamayyar kasa da kasa.

Me ya sa kasa da kasa suka soki shirin na Japan? Sabo da ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Ga shi kuma igiyar ruwa da ake samu a mashigar tekun Fukushima na da matukar karfi.

An ce da zaran an zubar da ruwan, zai iya bazuwa zuwa sama da rabin tekun Pasifik cikin kwanaki 57, da ma tekunan duniya baki daya cikin shekaru 10. Don haka, bai kamata a kawar da kai daga mummunan tasirin da zai iya haifarwa ga yanayin teku da ma tsaron abinci da kuma lafiyar bil Adama ba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Duk da haka, Japan ta yi ta kare aniyarta na aiwatar da shirin, tare da neman wanke kanta ta kowa ce hanya. Sai dai in da gaske ne ruwan dagwalon da take son zubarwa a cikin teku ba shi da illa, me ya hana kasar barin ruwa don yin amfani da shi wajen noma da sauran harkoki, ko kuma ta zuba su cikin tabkunanta?

Hakika, zubar da ruwan dagwalon ba batu ne da ya shafi kasar Japan ita kadai ba, batu ne da ya shafi duniya baki daya. Son kai na Japan ya iya haddasa hadari da ma illoli ga sauran kasashen duniya.

Yanzu haka, wata tawagar masana ta hukumar makamashin nukiliya ta duniya(IAEA) na yin ziyarar aiki ta kwanaki 5 a kasar ta Japan, muna fatan masanan na IAEA za su yi bincike kan wannan shiri na Japan bisa sanin ya kamata, da adalci, a kokarin kiyaye tsaron kasa da kasa.

Duniya na kalubalantar Japan da ta sauke nauyin da ke bisa wuyanta, ta yi cikakken shawarwari tare da masu ruwa da tsaki, don daidaita batun cikin tsaro kuma yadda ya kamata. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Ta Bai Wa Alhazan Jigawa Tabbacin Sauka Lafiya

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

43 minutes ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

2 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

4 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

5 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

12 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

13 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.