• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa kafin a fara aiwatar da duk wani irin aiki, dole ne a tantance ko ya dace ko bai dace ba, musamman ma game da muhimman ayyukan da ke shafar rayuka da lafiyar al’umma irinsu zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku.

  • Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Duk da haka, daga cikin dukkanin shirye-shirye da take iya zaba na sarrafa ruwan dagwalon, gwamnatin Japan ta zabi shirin zubar da ruwan cikin teku, saboda tsimin kudi da kuma rashin haifar da barazanar gurbacewar muhalli ga ita kanta, duk da hasarar da hakan ya haifarwa sauran kasashen duniya.

Idan ba a manta ba, a ranar 11 ga watan Maris na shekarar 2011, an yi girgizar kasa mai karfin maki 9 a tekun da ke arewa maso gabashin kasar ta Japan, girgizar da ta lalata tashar nukiliya ta Fukushima, har ma ta haddasa yoyon dimbin sinadaran nukiliya daga tashar. Ya zuwa shekarar 2021 kuma, gwamnatin Japan ta sanar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku bisa dalilinta na yadda ruwan ya kai iyakar da take iya adanawa, matakin da nan da nan ya jawo suka daga gamayyar kasa da kasa.

Me ya sa kasa da kasa suka soki shirin na Japan? Sabo da ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Ga shi kuma igiyar ruwa da ake samu a mashigar tekun Fukushima na da matukar karfi.

An ce da zaran an zubar da ruwan, zai iya bazuwa zuwa sama da rabin tekun Pasifik cikin kwanaki 57, da ma tekunan duniya baki daya cikin shekaru 10. Don haka, bai kamata a kawar da kai daga mummunan tasirin da zai iya haifarwa ga yanayin teku da ma tsaron abinci da kuma lafiyar bil Adama ba.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Duk da haka, Japan ta yi ta kare aniyarta na aiwatar da shirin, tare da neman wanke kanta ta kowa ce hanya. Sai dai in da gaske ne ruwan dagwalon da take son zubarwa a cikin teku ba shi da illa, me ya hana kasar barin ruwa don yin amfani da shi wajen noma da sauran harkoki, ko kuma ta zuba su cikin tabkunanta?

Hakika, zubar da ruwan dagwalon ba batu ne da ya shafi kasar Japan ita kadai ba, batu ne da ya shafi duniya baki daya. Son kai na Japan ya iya haddasa hadari da ma illoli ga sauran kasashen duniya.

Yanzu haka, wata tawagar masana ta hukumar makamashin nukiliya ta duniya(IAEA) na yin ziyarar aiki ta kwanaki 5 a kasar ta Japan, muna fatan masanan na IAEA za su yi bincike kan wannan shiri na Japan bisa sanin ya kamata, da adalci, a kokarin kiyaye tsaron kasa da kasa.

Duniya na kalubalantar Japan da ta sauke nauyin da ke bisa wuyanta, ta yi cikakken shawarwari tare da masu ruwa da tsaki, don daidaita batun cikin tsaro kuma yadda ya kamata. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Ta Bai Wa Alhazan Jigawa Tabbacin Sauka Lafiya

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

8 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

10 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

11 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

12 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.