• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba

by CMG Hausa
2 years ago
Japan

Sanin kowa ne cewa kafin a fara aiwatar da duk wani irin aiki, dole ne a tantance ko ya dace ko bai dace ba, musamman ma game da muhimman ayyukan da ke shafar rayuka da lafiyar al’umma irinsu zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku.

  • Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Duk da haka, daga cikin dukkanin shirye-shirye da take iya zaba na sarrafa ruwan dagwalon, gwamnatin Japan ta zabi shirin zubar da ruwan cikin teku, saboda tsimin kudi da kuma rashin haifar da barazanar gurbacewar muhalli ga ita kanta, duk da hasarar da hakan ya haifarwa sauran kasashen duniya.

Idan ba a manta ba, a ranar 11 ga watan Maris na shekarar 2011, an yi girgizar kasa mai karfin maki 9 a tekun da ke arewa maso gabashin kasar ta Japan, girgizar da ta lalata tashar nukiliya ta Fukushima, har ma ta haddasa yoyon dimbin sinadaran nukiliya daga tashar. Ya zuwa shekarar 2021 kuma, gwamnatin Japan ta sanar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku bisa dalilinta na yadda ruwan ya kai iyakar da take iya adanawa, matakin da nan da nan ya jawo suka daga gamayyar kasa da kasa.

Me ya sa kasa da kasa suka soki shirin na Japan? Sabo da ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Ga shi kuma igiyar ruwa da ake samu a mashigar tekun Fukushima na da matukar karfi.

An ce da zaran an zubar da ruwan, zai iya bazuwa zuwa sama da rabin tekun Pasifik cikin kwanaki 57, da ma tekunan duniya baki daya cikin shekaru 10. Don haka, bai kamata a kawar da kai daga mummunan tasirin da zai iya haifarwa ga yanayin teku da ma tsaron abinci da kuma lafiyar bil Adama ba.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Duk da haka, Japan ta yi ta kare aniyarta na aiwatar da shirin, tare da neman wanke kanta ta kowa ce hanya. Sai dai in da gaske ne ruwan dagwalon da take son zubarwa a cikin teku ba shi da illa, me ya hana kasar barin ruwa don yin amfani da shi wajen noma da sauran harkoki, ko kuma ta zuba su cikin tabkunanta?

Hakika, zubar da ruwan dagwalon ba batu ne da ya shafi kasar Japan ita kadai ba, batu ne da ya shafi duniya baki daya. Son kai na Japan ya iya haddasa hadari da ma illoli ga sauran kasashen duniya.

Yanzu haka, wata tawagar masana ta hukumar makamashin nukiliya ta duniya(IAEA) na yin ziyarar aiki ta kwanaki 5 a kasar ta Japan, muna fatan masanan na IAEA za su yi bincike kan wannan shiri na Japan bisa sanin ya kamata, da adalci, a kokarin kiyaye tsaron kasa da kasa.

Duniya na kalubalantar Japan da ta sauke nauyin da ke bisa wuyanta, ta yi cikakken shawarwari tare da masu ruwa da tsaki, don daidaita batun cikin tsaro kuma yadda ya kamata. (Lubabatu Lei)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.