• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Kamata A Bar Son Kan Japan Ya Shafi Kasashen Duniya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa kafin a fara aiwatar da duk wani irin aiki, dole ne a tantance ko ya dace ko bai dace ba, musamman ma game da muhimman ayyukan da ke shafar rayuka da lafiyar al’umma irinsu zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku.

  • Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Duk da haka, daga cikin dukkanin shirye-shirye da take iya zaba na sarrafa ruwan dagwalon, gwamnatin Japan ta zabi shirin zubar da ruwan cikin teku, saboda tsimin kudi da kuma rashin haifar da barazanar gurbacewar muhalli ga ita kanta, duk da hasarar da hakan ya haifarwa sauran kasashen duniya.

Idan ba a manta ba, a ranar 11 ga watan Maris na shekarar 2011, an yi girgizar kasa mai karfin maki 9 a tekun da ke arewa maso gabashin kasar ta Japan, girgizar da ta lalata tashar nukiliya ta Fukushima, har ma ta haddasa yoyon dimbin sinadaran nukiliya daga tashar. Ya zuwa shekarar 2021 kuma, gwamnatin Japan ta sanar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliya ta Fukushima a cikin teku bisa dalilinta na yadda ruwan ya kai iyakar da take iya adanawa, matakin da nan da nan ya jawo suka daga gamayyar kasa da kasa.

Me ya sa kasa da kasa suka soki shirin na Japan? Sabo da ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Ga shi kuma igiyar ruwa da ake samu a mashigar tekun Fukushima na da matukar karfi.

An ce da zaran an zubar da ruwan, zai iya bazuwa zuwa sama da rabin tekun Pasifik cikin kwanaki 57, da ma tekunan duniya baki daya cikin shekaru 10. Don haka, bai kamata a kawar da kai daga mummunan tasirin da zai iya haifarwa ga yanayin teku da ma tsaron abinci da kuma lafiyar bil Adama ba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

Duk da haka, Japan ta yi ta kare aniyarta na aiwatar da shirin, tare da neman wanke kanta ta kowa ce hanya. Sai dai in da gaske ne ruwan dagwalon da take son zubarwa a cikin teku ba shi da illa, me ya hana kasar barin ruwa don yin amfani da shi wajen noma da sauran harkoki, ko kuma ta zuba su cikin tabkunanta?

Hakika, zubar da ruwan dagwalon ba batu ne da ya shafi kasar Japan ita kadai ba, batu ne da ya shafi duniya baki daya. Son kai na Japan ya iya haddasa hadari da ma illoli ga sauran kasashen duniya.

Yanzu haka, wata tawagar masana ta hukumar makamashin nukiliya ta duniya(IAEA) na yin ziyarar aiki ta kwanaki 5 a kasar ta Japan, muna fatan masanan na IAEA za su yi bincike kan wannan shiri na Japan bisa sanin ya kamata, da adalci, a kokarin kiyaye tsaron kasa da kasa.

Duniya na kalubalantar Japan da ta sauke nauyin da ke bisa wuyanta, ta yi cikakken shawarwari tare da masu ruwa da tsaki, don daidaita batun cikin tsaro kuma yadda ya kamata. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Ta Bai Wa Alhazan Jigawa Tabbacin Sauka Lafiya

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Related

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

48 minutes ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

48 minutes ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

2 hours ago
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

3 hours ago
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro
Daga Birnin Sin

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

4 hours ago
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

23 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.