ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Matakin da shugaban Amurka ya dauka na katse mafi yawan tallafin da Amurka ke bai wa kasashe, ka iya haddasa mutuwar fiye da mutum miliyan 14 nan da 2030, kamar yadda binciken mujallar kiwon lafiya ta Lancet ya nuna.

Kashi uku cikin hudu na wadanda ke cikin hatsarin mutuwar kananan yara ne, a cewar binciken.

  • Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC
  • Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Kasashe masu karamin karfi da masu matsakaicin samu ne kan gaba wajen fuskantar barazanar katse tallafin.

ADVERTISEMENT

Ana kwatanta katse tallafin da annoba ko gagarumin yaki,” a cewar Dabide Rasella, wanda ke cikin wadanda suka wallafa rahoton.

A watan Maris Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ya ce an soke fiye da kashi 80 cikin 100 na duka shirye-shiryen hukumar bayar da agaji ta Amurka (USAID).

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

Shugaba Trump da abokansa sun ce sun gano cewa ana tafka almundahana da zamba a hukumar.

Rahoton na zuwa ne yayin da gomman shugabannin duniya ke taro a Birnin Sabeilla na kasar Sifaniya cikin makon nan domin tattauna batun katse tallafin, wanda ya fi kowane bayar da agaji a duniya.

Bayan nazarin bayanan alkaluman tallafin hukumar a kasashe 133 a duniya, binciken ya kiyasta cewa tallafin USAID ya rage mutuwar mutum miliyan 91 a kasashe masu tasowa tsakanin 2001 zuwa 2021.

Sun kuma yi amfani da wani kiyasi wajen hasashen yadda rage tallafin da kashi 83% adadin da gwamnatin Amurka ta sanar a farkon wannan shekara na iya shafar adadin masu mutuwa.

Rahoton ya ce katse tallafin zai haifar da mutuwar miliyan 14 nan da shekarar 2030.

Adadin ya kunshi yara fiye da miliyan 4.5 ‘yan kasa da shekara biyar, kwatankwacin mutuwar kananan yara 700,000 a kowace shekara.

Gwamnatin Trump karkashin sabuwar hukumar kula da kashe kudaden gwamnati, da a baya hamshakin attajirin nan Elon Musk ya jagoranta, ta kudiri aniyar rage kashe kudaden gwamnatin tarayya.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

September 16, 2026
Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose
Manyan Labarai

Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

September 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

September 16, 2026
Next Post
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d'Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Samar Da Hanyar Samun Wutar Lantarki A Kebbi Ta Wucin Gadi

TCN Ta Samar Da Hanyar Samun Wutar Lantarki A Kebbi Ta Wucin Gadi

September 16, 2026
APC Ta Tsawaita Rijistar Mambobinta, Ta Ɗage Ranar Babban Taronta Na Ƙasa

APC Ta Nemi A Gudanar Da Bincike Kan Farmakin Da A Kai Ofisoshinta A Kaduna

September 16, 2026
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Ban Taɓa Yi Wa Tinubu Alƙawarin Zan Koma APC Ba – Wike

September 16, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

September 16, 2026
Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

September 16, 2026
Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

September 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

September 16, 2026
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Gwamnati Ba Ta Da Hurumin Ɗaukar Nauyin Yi Wa Mutane Aure – Dino Melaye

September 16, 2026
An Bude Taron Kasa Da Kasa Karo Na 5 Dangane Da Tsarin Cin Gajiyar Fasahar Taurarin Dan Adam Na Beidou

An Bude Taron Kasa Da Kasa Karo Na 5 Dangane Da Tsarin Cin Gajiyar Fasahar Taurarin Dan Adam Na Beidou

September 15, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Harba Taurarin Dan Adam 10 Ta Amfani Da Rokar  Zhuque-2E

Sin Ta Yi Nasarar Harba Taurarin Dan Adam 10 Ta Amfani Da Rokar Zhuque-2E

September 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.