ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Matakin da shugaban Amurka ya dauka na katse mafi yawan tallafin da Amurka ke bai wa kasashe, ka iya haddasa mutuwar fiye da mutum miliyan 14 nan da 2030, kamar yadda binciken mujallar kiwon lafiya ta Lancet ya nuna.

Kashi uku cikin hudu na wadanda ke cikin hatsarin mutuwar kananan yara ne, a cewar binciken.

  • Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC
  • Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Kasashe masu karamin karfi da masu matsakaicin samu ne kan gaba wajen fuskantar barazanar katse tallafin.

ADVERTISEMENT

Ana kwatanta katse tallafin da annoba ko gagarumin yaki,” a cewar Dabide Rasella, wanda ke cikin wadanda suka wallafa rahoton.

A watan Maris Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ya ce an soke fiye da kashi 80 cikin 100 na duka shirye-shiryen hukumar bayar da agaji ta Amurka (USAID).

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Ɗaliban NECO A Borno

Shugaba Trump da abokansa sun ce sun gano cewa ana tafka almundahana da zamba a hukumar.

Rahoton na zuwa ne yayin da gomman shugabannin duniya ke taro a Birnin Sabeilla na kasar Sifaniya cikin makon nan domin tattauna batun katse tallafin, wanda ya fi kowane bayar da agaji a duniya.

Bayan nazarin bayanan alkaluman tallafin hukumar a kasashe 133 a duniya, binciken ya kiyasta cewa tallafin USAID ya rage mutuwar mutum miliyan 91 a kasashe masu tasowa tsakanin 2001 zuwa 2021.

Sun kuma yi amfani da wani kiyasi wajen hasashen yadda rage tallafin da kashi 83% adadin da gwamnatin Amurka ta sanar a farkon wannan shekara na iya shafar adadin masu mutuwa.

Rahoton ya ce katse tallafin zai haifar da mutuwar miliyan 14 nan da shekarar 2030.

Adadin ya kunshi yara fiye da miliyan 4.5 ‘yan kasa da shekara biyar, kwatankwacin mutuwar kananan yara 700,000 a kowace shekara.

Gwamnatin Trump karkashin sabuwar hukumar kula da kashe kudaden gwamnati, da a baya hamshakin attajirin nan Elon Musk ya jagoranta, ta kudiri aniyar rage kashe kudaden gwamnatin tarayya.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

MASU ALAKA

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

June 29, 2026
Yadda Yara Suka Kamo Harsasan Harbo Jirgin Sama A Yayin Kamun Kifi A Borno
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Ɗaliban NECO A Borno

June 29, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Tura Motocin CNG 40 Da Adaidaita Sahu 200 Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Motocin CNG 40 Da Adaidaita Sahu 200 Kano

June 29, 2026
Next Post
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d'Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

LABARAI MASU NASABA

Nuna Sha’awar Halartar Bikin CISCE Kowace Shekara

Nuna Sha’awar Halartar Bikin CISCE Kowace Shekara

June 29, 2026
Me Ya Sa Bikin CISCE Ya Zama Wajabi Domin Hadewa Da Makomar Gobe?

Me Ya Sa Bikin CISCE Ya Zama Wajabi Domin Hadewa Da Makomar Gobe?

June 29, 2026
Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki

Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki

June 29, 2026
Marwa Ya Kaddamar da Amfani da Bindigogin AK-47 Ga NDLEA

Marwa Ya Kaddamar da Amfani da Bindigogin AK-47 Ga NDLEA

June 29, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko

Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko

June 29, 2026
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Lalata Kilo12,234 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 29, 2026
CBN

Majalisa Ta Yi Tsit Yayin Da Gwamnati Ke Keta Haddin Amso Bashi – Sarkin Sanusi II

June 29, 2026
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

June 29, 2026
Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

June 29, 2026
Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

June 29, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.