ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Matakin da shugaban Amurka ya dauka na katse mafi yawan tallafin da Amurka ke bai wa kasashe, ka iya haddasa mutuwar fiye da mutum miliyan 14 nan da 2030, kamar yadda binciken mujallar kiwon lafiya ta Lancet ya nuna.

Kashi uku cikin hudu na wadanda ke cikin hatsarin mutuwar kananan yara ne, a cewar binciken.

  • Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC
  • Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Kasashe masu karamin karfi da masu matsakaicin samu ne kan gaba wajen fuskantar barazanar katse tallafin.

ADVERTISEMENT

Ana kwatanta katse tallafin da annoba ko gagarumin yaki,” a cewar Dabide Rasella, wanda ke cikin wadanda suka wallafa rahoton.

A watan Maris Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ya ce an soke fiye da kashi 80 cikin 100 na duka shirye-shiryen hukumar bayar da agaji ta Amurka (USAID).

LABARAI MASU NASABA

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

Shugaba Trump da abokansa sun ce sun gano cewa ana tafka almundahana da zamba a hukumar.

Rahoton na zuwa ne yayin da gomman shugabannin duniya ke taro a Birnin Sabeilla na kasar Sifaniya cikin makon nan domin tattauna batun katse tallafin, wanda ya fi kowane bayar da agaji a duniya.

Bayan nazarin bayanan alkaluman tallafin hukumar a kasashe 133 a duniya, binciken ya kiyasta cewa tallafin USAID ya rage mutuwar mutum miliyan 91 a kasashe masu tasowa tsakanin 2001 zuwa 2021.

Sun kuma yi amfani da wani kiyasi wajen hasashen yadda rage tallafin da kashi 83% adadin da gwamnatin Amurka ta sanar a farkon wannan shekara na iya shafar adadin masu mutuwa.

Rahoton ya ce katse tallafin zai haifar da mutuwar miliyan 14 nan da shekarar 2030.

Adadin ya kunshi yara fiye da miliyan 4.5 ‘yan kasa da shekara biyar, kwatankwacin mutuwar kananan yara 700,000 a kowace shekara.

Gwamnatin Trump karkashin sabuwar hukumar kula da kashe kudaden gwamnati, da a baya hamshakin attajirin nan Elon Musk ya jagoranta, ta kudiri aniyar rage kashe kudaden gwamnatin tarayya.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane
Manyan Labarai

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

June 9, 2026
ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir
Manyan Labarai

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
Next Post
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d'Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

June 9, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

Sin Da Afrika Ta Kudu Na Ci Gaba Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Soji

June 9, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

June 9, 2026
Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.