• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da baje kolin kasa da kasa na hajojin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE karo na 6 ke kara karatowa, yanzu haka sassan ’yan kasuwa, da masu ruwa da tsaki a hada hadar cinikayya daga bangarorin kasashen duniya daban daban, na kara nuna fatansu na halartar wannan muhimmin biki, ciki har da sassa da dama daga kasashen Afirka.

A baya bayan nan ma, wata tawaga karkashin hukumar yayatawa, da bunkasa cinikayya ta kasar Zimbabwe mai lakabin “ZimTrade”, ta bayyana shirya ta na halartar wannan baje koli, kunshe da wakilai daga kamfanoni sama da 15.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Cikakken ‘Yancin Kan Kasar Sudan
  • Kyawawan Manufofin Tattalin Arzikin Sin Na Kara Karfafawa Kamfanonin Ketare Gwiwar Shiga Babbar Kasuwar Kasar

To ko me ya sa bikin baje kolin na CIIE dake gudana a birnin Shanghai, wanda kuma a bana za a yi tsakanin ranaikun 5 zuwa 10 ga watan Nuwamba ke jan hankalin ’yan kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki? Ko shakka babu amsar wannan tambaya shi ne tagomashin da bikin ke da shi ta fuskar samar da babbar dama, ta yin cudanya, da karfafawa ko kulla sabbin alakokin cinikayya tsakanin mahalartansa.

Baje kolin na CIIE ya zamo wani babban dandali na baiwa ’yan kasuwa damar gano abubuwan da babbar kasuwar kasar Sin ke bukata, da zakulo damammakin cinikayya masu inganci ga dukkanin sassa.

Ga tawagar “ZimTrade” ta kasar Zimbabwe, a wannan karo ta shirya zuwa baje kolin na CIIE tare da wakilan kamfanonin sarrafa fatu, da na na sarrafa abinci, da masu sana’o’in fasahohin hannu, da kamfannonin sadarwar tarho, da na hakar ma’adanai. Sauran su ne na makamashi da kuma na yawon bude ido.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Masharhanta na kallon baje kolin na wannan karo a matsayin wata dama, ta yaukaka alakar cinikayya tsakanin Sin da Zimbabwe, wadda a baya bayan nan ke kara fadada, inda ta kai kasar Sin din zama ta uku mafi karbar hajojin da Zimbabwe ke fitarwa ketare cikin shekaru 3 da suka gabata.

Baje kolin CIIE, ya ci gaba da kasance muhimmin dandali na kyautata fahimtar juna tsakanin ’yan kasuwa, kasancewarsa mafi girma a fanin baiwa masu ruwa da tsaki damar nazartar tsarin Sin na kara bude kofa ga waje, da shigar da hajoji cikin babbar kasuwar kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ilawaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Hana Amurka Ta Ce “A Tsagaita Bude Wuta”?

Next Post

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

12 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

14 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

14 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

15 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

16 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

18 hours ago
Next Post
Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami'ar Bayero — Hassan Baita

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.