ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
CIIE

Yayin da baje kolin kasa da kasa na hajojin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE karo na 6 ke kara karatowa, yanzu haka sassan ’yan kasuwa, da masu ruwa da tsaki a hada hadar cinikayya daga bangarorin kasashen duniya daban daban, na kara nuna fatansu na halartar wannan muhimmin biki, ciki har da sassa da dama daga kasashen Afirka.

A baya bayan nan ma, wata tawaga karkashin hukumar yayatawa, da bunkasa cinikayya ta kasar Zimbabwe mai lakabin “ZimTrade”, ta bayyana shirya ta na halartar wannan baje koli, kunshe da wakilai daga kamfanoni sama da 15.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Cikakken ‘Yancin Kan Kasar Sudan
  • Kyawawan Manufofin Tattalin Arzikin Sin Na Kara Karfafawa Kamfanonin Ketare Gwiwar Shiga Babbar Kasuwar Kasar

To ko me ya sa bikin baje kolin na CIIE dake gudana a birnin Shanghai, wanda kuma a bana za a yi tsakanin ranaikun 5 zuwa 10 ga watan Nuwamba ke jan hankalin ’yan kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki? Ko shakka babu amsar wannan tambaya shi ne tagomashin da bikin ke da shi ta fuskar samar da babbar dama, ta yin cudanya, da karfafawa ko kulla sabbin alakokin cinikayya tsakanin mahalartansa.

ADVERTISEMENT

Baje kolin na CIIE ya zamo wani babban dandali na baiwa ’yan kasuwa damar gano abubuwan da babbar kasuwar kasar Sin ke bukata, da zakulo damammakin cinikayya masu inganci ga dukkanin sassa.

Ga tawagar “ZimTrade” ta kasar Zimbabwe, a wannan karo ta shirya zuwa baje kolin na CIIE tare da wakilan kamfanonin sarrafa fatu, da na na sarrafa abinci, da masu sana’o’in fasahohin hannu, da kamfannonin sadarwar tarho, da na hakar ma’adanai. Sauran su ne na makamashi da kuma na yawon bude ido.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Masharhanta na kallon baje kolin na wannan karo a matsayin wata dama, ta yaukaka alakar cinikayya tsakanin Sin da Zimbabwe, wadda a baya bayan nan ke kara fadada, inda ta kai kasar Sin din zama ta uku mafi karbar hajojin da Zimbabwe ke fitarwa ketare cikin shekaru 3 da suka gabata.

Baje kolin CIIE, ya ci gaba da kasance muhimmin dandali na kyautata fahimtar juna tsakanin ’yan kasuwa, kasancewarsa mafi girma a fanin baiwa masu ruwa da tsaki damar nazartar tsarin Sin na kara bude kofa ga waje, da shigar da hajoji cikin babbar kasuwar kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami'ar Bayero — Hassan Baita

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.