• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da baje kolin kasa da kasa na hajojin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE karo na 6 ke kara karatowa, yanzu haka sassan ’yan kasuwa, da masu ruwa da tsaki a hada hadar cinikayya daga bangarorin kasashen duniya daban daban, na kara nuna fatansu na halartar wannan muhimmin biki, ciki har da sassa da dama daga kasashen Afirka.

A baya bayan nan ma, wata tawaga karkashin hukumar yayatawa, da bunkasa cinikayya ta kasar Zimbabwe mai lakabin “ZimTrade”, ta bayyana shirya ta na halartar wannan baje koli, kunshe da wakilai daga kamfanoni sama da 15.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Cikakken ‘Yancin Kan Kasar Sudan
  • Kyawawan Manufofin Tattalin Arzikin Sin Na Kara Karfafawa Kamfanonin Ketare Gwiwar Shiga Babbar Kasuwar Kasar

To ko me ya sa bikin baje kolin na CIIE dake gudana a birnin Shanghai, wanda kuma a bana za a yi tsakanin ranaikun 5 zuwa 10 ga watan Nuwamba ke jan hankalin ’yan kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki? Ko shakka babu amsar wannan tambaya shi ne tagomashin da bikin ke da shi ta fuskar samar da babbar dama, ta yin cudanya, da karfafawa ko kulla sabbin alakokin cinikayya tsakanin mahalartansa.

Baje kolin na CIIE ya zamo wani babban dandali na baiwa ’yan kasuwa damar gano abubuwan da babbar kasuwar kasar Sin ke bukata, da zakulo damammakin cinikayya masu inganci ga dukkanin sassa.

Ga tawagar “ZimTrade” ta kasar Zimbabwe, a wannan karo ta shirya zuwa baje kolin na CIIE tare da wakilan kamfanonin sarrafa fatu, da na na sarrafa abinci, da masu sana’o’in fasahohin hannu, da kamfannonin sadarwar tarho, da na hakar ma’adanai. Sauran su ne na makamashi da kuma na yawon bude ido.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Masharhanta na kallon baje kolin na wannan karo a matsayin wata dama, ta yaukaka alakar cinikayya tsakanin Sin da Zimbabwe, wadda a baya bayan nan ke kara fadada, inda ta kai kasar Sin din zama ta uku mafi karbar hajojin da Zimbabwe ke fitarwa ketare cikin shekaru 3 da suka gabata.

Baje kolin CIIE, ya ci gaba da kasance muhimmin dandali na kyautata fahimtar juna tsakanin ’yan kasuwa, kasancewarsa mafi girma a fanin baiwa masu ruwa da tsaki damar nazartar tsarin Sin na kara bude kofa ga waje, da shigar da hajoji cikin babbar kasuwar kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ilawaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Hana Amurka Ta Ce “A Tsagaita Bude Wuta”?

Next Post

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Related

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo
Daga Birnin Sin

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

1 hour ago
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

18 hours ago
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

19 hours ago
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

20 hours ago
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

22 hours ago
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

23 hours ago
Next Post
Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami'ar Bayero — Hassan Baita

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.