ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

by Leadership Hausa
3 years ago
Jami'ar Bayero

Tsofaffin Ɗaliban Sashen Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero ‘yan ajin shekarar karatu ta 2011 zuwa 2015 sun sha alwashin sabunta ɗakin karatu na sashen wanda aka fi sani da Ɗakin Karatu Na Farfesa MAZ Sani.

Shugaban tawagar tsofaffin ɗaliban, Alh. Hassan Baita Ubawaru, ne ya bayyana haka yayin da ya ke miƙa wasu sababbin injinan naɗar takardu (Photocopy) guda uku da ya gwangwaje sashen nasu a madadin ɗaliban a matsayin gudunmawarsu don sauƙaƙa harkokin koyo da koyarwa a sashen a ranar Alhamis 02, ga watan Nuwambar 2023.

Injinan Nadar Takardu Uku Da Tsofaffin Daliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Suka Suka Ba BUK
Injinan Naɗar Takardu Uku Da Tsofaffin Ɗaliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Suka Suka Ba BUK
  • Jami’ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu
  • Tsohon Shugaban Jam’iar Bayero Ta Kano, Farfesa Ibrahim Umar Ya Rasu

Da yake miƙa injinan, Alh. Hassan Baita, wanda shi ne shugaban taron sada zumunci na ‘yan ajin shekarar 2015 kuma wanda ya ɗauki nauyan sayan injinan ya ce, wannan somun-taɓi ne kuma lokaci bayan lokaci za a ke irin waɗannan ayyuka don bunƙasa wannan sashe.

ADVERTISEMENT
Tsofaffin Daliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Yayin Mika Injinan Nadar Takardu A BUK
Tsofaffin Ɗaliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Yayin Miƙa Injinan Naɗar Takardu A BUK

A nasa jawabin, tsohon Sakataren Ƙungiyar Hausa ta Jami’ar Bayero, Muhammad Bashir Amin, ya bayyana ƙudurinsu na bunƙasa sashen ta hanyar bijiro da ayyukan da za su ciyar da sashen gaba, ya kuma buƙaci malamai da su ƙara kyautata alaƙarsu da ɗalibansu su ja su a jika, su ɗauke su tamkar ‘ya’yan da suka haifa, saboda hakan zai ƙara yi wa ɗaliban ƙaimi wajen tunawa da su bayan Allah ya ɗaukaka su a rayuwa.

Shugaban Sashen, Farfesa Isah Mukhtar, ya godewa ɗaliban da suka yi wannan hoɓɓasa da abun arziƙi a lokacin da ya ke shugabantar sashen, ya kuma bayyana cewa haƙiƙa irin wannan tallafi zai taimaka musu su tsallake tantancewar hukumar kula da Jami’o’i ta ƙasa da za ta yi wa sashen a shekara mai zuwa, wanda gaza samar da kayan koyo da koyarwa da kayan gudanar da aiki ka iya kaiwa ga samun babbar matsalar da zata iya kaiwa ga rufe sashen baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Taron ya samu halartar mataimakin shugaban tsangayar fasaha da nazarin addinin musulunci da malaman sashen yayin bikin miƙa injinan.

Mahalarta taron daga ɓangaren malamai da ɗalibai sun jinjinawa ƙoƙarin tsofaffin ɗaliban na samar da injinan, sun kuma gode musu da fatan Allah ya yalwata arziƙinsu.

Jami'ar Bayero
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al’umma

Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al'umma

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.