Mutane kusan bakwai sun rasu bayan wani ya tarwatse a ƙauyen Gwabro da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, a lokacin da waɗanda abin ya rutsa da su ke dawowa daga yawon Sallah a kan babura.
- Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya
- Kididiga Ta Nuna Yadda Kasar Sin Ke Samun Bunkasar Tattalin Arzikin Teku
Rahotanni sun nuna cewa an dasa bama-baman ne a ƙarƙashin wata itaciya da sojoji ke amfani da ita a matsayin wajen hutu yayin sintiri.
Bayan fashewar, mutum shida sun mutu nan take, yayin da ɗaya daga cikin yara biyu da suka jikkata ta rasu washegari.
Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza, Alhaji Ghazzali Rakah, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa waɗanda suka mutu mazauna ƙauyen Zurmuku ne, wanda ke maƙwabtaka da inda lamarin ya faru.
A baya, irin wannan mummunan abu ya faru a yankin, inda sojoji da dama suka rasa rayukansu sakamakon fashewar bama-bamai.
Hakan na ƙara nuna irin barazanar da matsalar tsaro ke ci gaba da haifarwa a Jihar Sakkwato, inda mazauna ke roƙon gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen kawo ƙarshen hare-haren ‘yan ta’adda, musamman masu tayar da bama-bamai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp