A ƙalla mutane huɗu sun mutu yayin da wasu 21 suka jikkata sakamakon fashewar bama-bamai biyu da ‘yan ta’addar ISWAP suka dasa a ƙaramar hukumar Gujba ta jihar Yobe.
Fashewar ta farko ta faru ne da safiyar ranar Juma’a a hanyar Goniri-Buni Yadi, inda wata motar kasuwanci da ke ɗaukar ƴan kasuwa zuwa kasuwar Buni Yadi ta taka wani bam da aka dasa kusa da ƙauyen Bultaram.
- Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe
- Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe
Mutane uku sun mutu a asibitin kwararru na jihar Yobe da ke Damaturu, yayin da wasu 21 ke ci gaba da jinya.
Ƴan sa’o’i bayan haka, wani ɗan keke da ba a san ko wanene ba ya taka wani bam a yankin, inda ya mutu a asibitin Buni Yadi.
Jami’an tsaro da na agajin gaggawa sun yi aikin share hanya don hana ƙarin ɓarna, yayin da aka ci gaba da binciken yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp