• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Fara Rubutu Don Daukaka Ko Neman Shahara Ba – Maimuna Tijjani

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adabi
0
Ban Fara Rubutu Don Daukaka Ko Neman Shahara Ba – Maimuna Tijjani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maimuna Tijjani Iyam na daya daga cikin marubutan littattafan Hausa a yanar gizo masu tasowa. A ttaunawarta da Wakiliyarmu Princess Fatima Zarah Mazadu ta bayyanawa masu karatu dalilin da ya sa ta fara rubutu har ma da bangaren da ta fi karkata wajen yin rubutun, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai Yadda tattaunawar ta kasance:

Masu karatu za su so su ji cikakken sunanki?

Sunana Maimuna Tijjani Iyam

 

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Da farko kamar yadda na fada sunana Maimuna Tijjani Iyam haifaffiyar jihar Yobe cikin karamar hukumar Potiskum, a nan nayi makaranta tun daga kan ‘Nursery School’ har yanzu da nake matakin kama da ‘Secondary’ ina karatu a ‘Federal College Of Education Potiskum’ ina karantar ‘Computer/Biology’.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?

Gaskiya tun ina karama na tashi da sha’awar rubutu da kuma karance-karance, tun ba iya rubutun hausa ba nake kwatanta rubuta labari ta hanyar zanen hoto har na iya, a takaice dai sha’awa da son ba wa al’ummata gudumawa shi ya ja hankali na tsunguma harkar rubutu.

 

Za ki shekara nawa da fara rubutu?

Na fara rubutu tun ina aji uku a ‘Primary’ tun lokacin hausar bata gama zauna mini dai-dai ba wajen rubutata a rubuce.

 

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

An sha gwagwarmaya amma yanzu Alhamdulillah, matsalar farko da na fara cin karo da ita shi ne kafin a amince mini a gida na fara rubutun kasancewar karancin shekaruna a lokacin.

 

Kina so ki ce iyayenki ba su amince da fara rubutunki ba?

Gaskiya an nuna rashin amincewa don cikin wasa na fara sanar da mahaifiyata amma sai ta nuna mini bata so, duk da ita ma ma’abociyar karance-karance sosai, sai daga baya kuma na samu amincewar su wanda yanzu Alhamdulillahi.

 

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutu?

Na fi mai da hankali game da abubuwan da suke faruwa a rayuwar mu ta yau da kullum, kuma duk wanda ya karanta littafina ya san hakan, gaskiya ban fiye gina jigon labari cakocam akan soyayya ba.

Kin rubuta labari sun kai kamar guda nawa?

Labarai biyar gare ni daga lokacin da na fara zuwa yanzu daan lokacin dana fara ina rubutawa a takarda kafin na mallaki waya na rasa da yawa daga cikinsu.

 

Ya farkon farawarki ya kasance?

Gaskiya farkon fara rubutuna bai zo mini da wata matsala ba, kasancewar kafin na fara na zurfafa bincike sosai a harkar, har na tsinci wasu ilmin tun kafin na ma fara.

 

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa?

‘Matan Arewa’ Gaskiya shi ya fi bani wahala, domin rubutu ne mai fadi sosai da ya kunshi abubuwa da yawa musamman akan mata da irin rayuwar da suke fuskanta a arewa.

 

Kin taba buga labarinki?

A’a babu sai dai niyya.

 

Wanne irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdulillah na samu nasarori sosai musamman addu’o’in jama’a, na dauki hakan babban nasarar da kudi ba za su saya min su ba.

 

Ya ki ka dauki rubutu a wajenki?

Na dauki rubutu wata hanyar isar da sako ga jama’a mai cike da hikima.

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Burina a rubutu shi ne sakon da nake son isarwa su kai inda kafafuna ko muryata basu da damar zuwa, domin ban fada harkar rubutu don zama sananniya ko kuma domin bidar shahara ba, illa iyaka son bada tawa gudumawar ga al’umma ta hanyar ruwan alkalamina.

 

Bayan rubutu kina wata sana’ar?

Eh! ina harkan ‘Graphics’.

 

Ya ki ke iya hada rubutunki da kuma sana’arki?

Kowanne da lokacinsa kuma babu wanda yake shiga lokacin wani.

 

Kamar da wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

Safe da kuma yammaci don sam bana yin rubutu da rana.

 

Me za ki ce da masoyanki?

Babu abin da zance dasu face godiya na gode da soyayyarsu gare ni Allah ya bar zumunci da kauna tsakaninmu.

 

Ko kinada wadanda za ki gaisar?

Da farko iyayena Alh.Tijjani Iyam da kuma malama Aisha Ishak Fada, sai kuma Ahmad Toshiba wanda ya zamto tamkar dan uwan da muka fito ciki daya dashi wanda harkar rubutu ce ta hada mu, sai kuma ‘yan uwa da abokan arziki da makaranta littattafaina


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Kaddamar Da Taro Na Biyu Na Majalisar CPPCC Karo Na 14 Gobe Litinin

Next Post

Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

4 weeks ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

5 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

6 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

6 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

6 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

8 months ago
Next Post
Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 16/05/2025

GORON JUMA’A 16/05/2025

May 16, 2025
Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

May 16, 2025
Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

May 16, 2025
Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.