• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Fara Rubutu Don Daukaka Ko Neman Shahara Ba – Maimuna Tijjani

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Maimuna Tijjani

Maimuna Tijjani Iyam na daya daga cikin marubutan littattafan Hausa a yanar gizo masu tasowa. A ttaunawarta da Wakiliyarmu Princess Fatima Zarah Mazadu ta bayyanawa masu karatu dalilin da ya sa ta fara rubutu har ma da bangaren da ta fi karkata wajen yin rubutun, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai Yadda tattaunawar ta kasance:

Masu karatu za su so su ji cikakken sunanki?

Sunana Maimuna Tijjani Iyam

 

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Da farko kamar yadda na fada sunana Maimuna Tijjani Iyam haifaffiyar jihar Yobe cikin karamar hukumar Potiskum, a nan nayi makaranta tun daga kan ‘Nursery School’ har yanzu da nake matakin kama da ‘Secondary’ ina karatu a ‘Federal College Of Education Potiskum’ ina karantar ‘Computer/Biology’.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?

Gaskiya tun ina karama na tashi da sha’awar rubutu da kuma karance-karance, tun ba iya rubutun hausa ba nake kwatanta rubuta labari ta hanyar zanen hoto har na iya, a takaice dai sha’awa da son ba wa al’ummata gudumawa shi ya ja hankali na tsunguma harkar rubutu.

 

Za ki shekara nawa da fara rubutu?

Na fara rubutu tun ina aji uku a ‘Primary’ tun lokacin hausar bata gama zauna mini dai-dai ba wajen rubutata a rubuce.

 

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

An sha gwagwarmaya amma yanzu Alhamdulillah, matsalar farko da na fara cin karo da ita shi ne kafin a amince mini a gida na fara rubutun kasancewar karancin shekaruna a lokacin.

 

Kina so ki ce iyayenki ba su amince da fara rubutunki ba?

Gaskiya an nuna rashin amincewa don cikin wasa na fara sanar da mahaifiyata amma sai ta nuna mini bata so, duk da ita ma ma’abociyar karance-karance sosai, sai daga baya kuma na samu amincewar su wanda yanzu Alhamdulillahi.

 

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutu?

Na fi mai da hankali game da abubuwan da suke faruwa a rayuwar mu ta yau da kullum, kuma duk wanda ya karanta littafina ya san hakan, gaskiya ban fiye gina jigon labari cakocam akan soyayya ba.

Kin rubuta labari sun kai kamar guda nawa?

Labarai biyar gare ni daga lokacin da na fara zuwa yanzu daan lokacin dana fara ina rubutawa a takarda kafin na mallaki waya na rasa da yawa daga cikinsu.

 

Ya farkon farawarki ya kasance?

Gaskiya farkon fara rubutuna bai zo mini da wata matsala ba, kasancewar kafin na fara na zurfafa bincike sosai a harkar, har na tsinci wasu ilmin tun kafin na ma fara.

 

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa?

‘Matan Arewa’ Gaskiya shi ya fi bani wahala, domin rubutu ne mai fadi sosai da ya kunshi abubuwa da yawa musamman akan mata da irin rayuwar da suke fuskanta a arewa.

 

Kin taba buga labarinki?

A’a babu sai dai niyya.

 

Wanne irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdulillah na samu nasarori sosai musamman addu’o’in jama’a, na dauki hakan babban nasarar da kudi ba za su saya min su ba.

 

Ya ki ka dauki rubutu a wajenki?

Na dauki rubutu wata hanyar isar da sako ga jama’a mai cike da hikima.

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Burina a rubutu shi ne sakon da nake son isarwa su kai inda kafafuna ko muryata basu da damar zuwa, domin ban fada harkar rubutu don zama sananniya ko kuma domin bidar shahara ba, illa iyaka son bada tawa gudumawar ga al’umma ta hanyar ruwan alkalamina.

 

Bayan rubutu kina wata sana’ar?

Eh! ina harkan ‘Graphics’.

 

Ya ki ke iya hada rubutunki da kuma sana’arki?

Kowanne da lokacinsa kuma babu wanda yake shiga lokacin wani.

 

Kamar da wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

Safe da kuma yammaci don sam bana yin rubutu da rana.

 

Me za ki ce da masoyanki?

Babu abin da zance dasu face godiya na gode da soyayyarsu gare ni Allah ya bar zumunci da kauna tsakaninmu.

 

Ko kinada wadanda za ki gaisar?

Da farko iyayena Alh.Tijjani Iyam da kuma malama Aisha Ishak Fada, sai kuma Ahmad Toshiba wanda ya zamto tamkar dan uwan da muka fito ciki daya dashi wanda harkar rubutu ce ta hada mu, sai kuma ‘yan uwa da abokan arziki da makaranta littattafaina

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)
Adabi

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

April 19, 2025
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

December 30, 2024
Next Post
Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

Shugaban Kasar Saliyo Na Fatan Hadin Gwiwar Aikin Gona Da Lardin Hubei Na Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.