• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

by Khalid Idris Doya
3 months ago
in Labarai
0
Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bankin Duniya ya shirya tsaf domin amincewa da sabon rokon cin bashin dala miliyan 632 da Nijeriya ke nema a daidai kabar da ake ta kukan yawan basukan da ke kan kasar ma sun yi yawa. 

Rancen wanda aka shirya ciwo shi domin taimaka wa bangarorin da suka hada da inganta sashin abinci mai gina jiki da samar da ilimi mai inganci a matakin farko.

  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu
  • Dubban Jama’a Sun Sallaci Gawar Sheikh Idris Dutsen Tanshi

A bayanan da aka samu a shafin bankin dukiyar a ranar Lahadi, ya nuna cewa rancen ya kunshi na dala miliyan 80 da aka ware domin inganta sashin samar da abinci mai gina jikin dan’adam a Nijeriya a shiri na 2.0 da kuma wani rancen dala miliyan 552 da aka nema domin shiri mai hankoron samar da ingancin ilimi a matakin farko ga kowa.

Wannan matakin dai dukkan suna karkashin shirin babban bankin na taimaka wa Nijeriya a bangaren shirinta na samar da ci gaba da suke da manufar kyautata lafiya, ilimi da ci gaban jama’a.

Rancen ana sa ran za su taimaka wa kokarin gwamnatin tarayya na inganta samar da abinci mai gina jiki da kuma inganta samun damar ilimi mai inganci ga yara kanana a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

A halin da ake ciki, tuni ma Bankin Duniya ya riga ya amince da lamunin dala miliyan 500 ga Nijeriya a ranar Juma’ar da ta gabata don tallafa wa shirin kasar na “Community Action for Resilience and Economic Stimulus Programme”.

Samun wannan rancen wani dama ce ga Nijeriya da zai taimaka mata wajen shawo kan matsalolin da suke bangaren tattalin arziki da inganta yanayin rayuwar jama’a, wadata kasa da abinci, da samar da range ga talakawa da kamfanoni.

Kazalika, a wani rancen da Nijeriya ta nema na dala miliyan 800 domin shirin ‘National Social Safety-Net Program Scale Up,’ Bankin Duniyan ya sake wa Nijeriya dala miliyan 315 daga cikin wannan adadin.

Tsawon kusan shekara, Nijeriya ba ta samu wani kudi daga Babban Bankin duniya ba a matsayin rance, tun bayan wanda ta ba ta a watan Disamban 2021. Na samu jinkirin sake kudaden ne sakamakon wasu batutuwa na damfara da aka gano a shirin.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar da shirin SSN wanda ke da manufar rabar da naira dubu 25,000 ga magidanta miliyan 15 na tsawon watanni uku domin yaki da fatara. Ma’aikatar kula da jin kai da yaki da talauci ne aka daura wa alhakin gudanar da shirin rancen dala miliyan 800 na Bankin Duniyan.

Har ila yau, gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin tallafin kudi na (cash transfer programme) domin gudanar da bincike kan zarge-zargen almundahana da ke makale da shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalaDuniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira

Next Post

APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

Related

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata
Labarai

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

43 minutes ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

5 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

8 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

9 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

11 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

12 hours ago
Next Post
APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

July 9, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

July 9, 2025
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.