• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin TAJ Ya Kafa Sabon Tarihi A Harkokin Bankin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Bankin TAJ Ya Kafa Sabon Tarihi A Harkokin Bankin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bankin TAJ mai gudanar da harkokinsa da ke bunkasa cikin sauri ta hanyar fasaha, ya kafa sabon tarihi sama da shekara 100 ba a samu irinsa ba.

A cikin shekaru uku da kafa Bankin TAJ, ya samu nasarar biyan riba ga masu hannun jari.

  • A Karon Farko Sanata Barau Ya Jagoranci Zaman Majalisar Dattawan Nijeriya
  • Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Idan za a iya tunawa, Bankin TAJ ya kafa tarihi a farkon wannan shekarar a matsayin bankin na farko a tarihin Nijeriya da ya jera tsarin manuni na Sukuk a kan kasuwar hada-hadar kudi ta Nijeriya bayan samun nasarar fitar da shi.

Bayanan da aka samu daga rahoton kudade na bankin kasuwanci ya nuna cewa babu wani banki da ya samu irin wannan gagarumin nasara irin wannan a cikin sama da shekaru 100 na tarihin harkokin kudade.

Da yake jawabi ga masu hannun jarin a wajen taron, shugaban gudanarwar bankin, Alhaji Tanko Isiaku Gwamna, ya ba da labarin guguwar tattalin arzikin duniya a cikin shekaru biyu da suka gabata, da kuma ci gaban tattalin arzikin kasa da aka samu a fanni, musamman hauhawar farashin kayayyaki wanda ya yi illa ga harkokin kasuwanci.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gwamna ya ci gaba da cewa, duk da yanayin da ake ciki na rashin aikin yi, hukumar gudanarwar bankin za su yi kokarin kirkiro da dabaru masu muhimmanci da za su ci gaba da dora Bankin TAJ a kan turbar da ta tace domin amfanin masu hannun jari da kuma tattalin arzikin Nijeriya.

Dangane da batun rabon ribar, ya ce, “A madadin hukumar gudanarwa, ina farin cikin sanar da masu hannun jarinmu cewa mun ba da shawarar a biya rarar kashi 1 ga kowane hannun jari 10, bisa amincewar masu hannun jari. Za mu ci gaba da jajircewa wajen inganta fadada kasuwanci da samun nasara tare da tabbatar da cewa an kebe maku adadi mai yawa na ribar da muka samu.”

A cikin rahotonsa, shugaban bankin, Mista Hamid Joda, ya bayyana cewa harkokin kudade a 2022 yana da matukar muhimmi ga ci gaba a cikin tafiyar masu ba da bashi babu ruwa duk da irin kalubalen da aka samu na nuna yanayin aiki, amma an samu nasarar cimma abubuwa masu yawa.

Dangane da harkokin kudade na bankin a cikin 2022, Joda ya ruwaito cewa Bankin TAJ ya samu karuwa a cikin muhimman abubuwa a shekarar, yayin da ma’auni ya karu da sama da 93 daga Naira biliyan 110 da aka samu na 2021 zuwa Naira biliyan 212, yayin da riba kafin fitar da haraji ya karu daga Naira biliyan 1.6 a 2021 zuwa Naira biliyan 5.081 biliyan a shekarar kudi ta 2022.

Ya kuma shaida wa masu hannun jarin cewa ribar da bankin ke samu a kowanne kaso ya karu da kashi 138 zuwa Naira 31.27 a 2022, idan aka kwatanta da Naira 13.11 da aka samu a shekarar 2021.

Game da shirye-shiryen kara bunkasa harkokin bankin nan da shekaru masu zuwa kuwa, Joda ya ce, “A kokarin da muke yi na inganta kayayyakin da ake samu ribar da babu ruwa da kuma tsarin hada-hadar banki a duk fadin kasar nan, hukumar gudanarwar ta Bankin TAJ sun kafa muhimman manufofi da za a bi a shekarar 2023.

“Muna shirin bude rassa da ofisoshin kasuwanci 110 a fadin manyan biranen jihohi da manyan cibiyoyin kasuwanci kafin shekarar 2024 da kuma bayar da kayayyaki da ayyuka na banki da babu ruwa ga kasuwanni, domin habaka hanyar sadarwar hukumarmu zuwa wakilai masu aiki 100,000 nan da 2025, don rage matsalolin harkokin kudi tare da habaka abokanan kasuwanci zuwa akalla miliyan hudu nan da 2027, saboda cimma bukatar mafi karancin gamsuwar abokin ciniki na kashi 85,” in ji shi.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan taron, kwararre kan harkokin kudi, Alhaji Tata Shekaru Omar, ya yaba wa hukumar gudanarwa bisa sabbin tsare-tsare da suka sanya har Bankin TAJ ya zama na sahun gaba a harkokin hada-hadar kudi na kasar nan.

Ya ce, “Bankin TAJ bai cika shekara hudu da kafawa ba, amma ya samu gagarumar riba a shekararsa ta farko da ya fara aiki, labari ne mai dadi da farin ciki ga duk masu hannun jari a bankin. Ina so in yi godiya ga shugaban bankin da daukacin tawagarsa da suka yi irin wannan aiki, musamman yadda bankin ke ba da riba ga masu hannun jari.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bankin TajNasara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Bude Shafi A Sabuwar Manhajar Threads Kishiyar Twitter

Next Post

Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

48 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama

Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.