ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin TAJ Ya Kafa Sabon Tarihi A Harkokin Bankin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
TAJ

Bankin TAJ mai gudanar da harkokinsa da ke bunkasa cikin sauri ta hanyar fasaha, ya kafa sabon tarihi sama da shekara 100 ba a samu irinsa ba.

A cikin shekaru uku da kafa Bankin TAJ, ya samu nasarar biyan riba ga masu hannun jari.

  • A Karon Farko Sanata Barau Ya Jagoranci Zaman Majalisar Dattawan Nijeriya
  • Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Idan za a iya tunawa, Bankin TAJ ya kafa tarihi a farkon wannan shekarar a matsayin bankin na farko a tarihin Nijeriya da ya jera tsarin manuni na Sukuk a kan kasuwar hada-hadar kudi ta Nijeriya bayan samun nasarar fitar da shi.

ADVERTISEMENT

Bayanan da aka samu daga rahoton kudade na bankin kasuwanci ya nuna cewa babu wani banki da ya samu irin wannan gagarumin nasara irin wannan a cikin sama da shekaru 100 na tarihin harkokin kudade.

Da yake jawabi ga masu hannun jarin a wajen taron, shugaban gudanarwar bankin, Alhaji Tanko Isiaku Gwamna, ya ba da labarin guguwar tattalin arzikin duniya a cikin shekaru biyu da suka gabata, da kuma ci gaban tattalin arzikin kasa da aka samu a fanni, musamman hauhawar farashin kayayyaki wanda ya yi illa ga harkokin kasuwanci.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Gwamna ya ci gaba da cewa, duk da yanayin da ake ciki na rashin aikin yi, hukumar gudanarwar bankin za su yi kokarin kirkiro da dabaru masu muhimmanci da za su ci gaba da dora Bankin TAJ a kan turbar da ta tace domin amfanin masu hannun jari da kuma tattalin arzikin Nijeriya.

Dangane da batun rabon ribar, ya ce, “A madadin hukumar gudanarwa, ina farin cikin sanar da masu hannun jarinmu cewa mun ba da shawarar a biya rarar kashi 1 ga kowane hannun jari 10, bisa amincewar masu hannun jari. Za mu ci gaba da jajircewa wajen inganta fadada kasuwanci da samun nasara tare da tabbatar da cewa an kebe maku adadi mai yawa na ribar da muka samu.”

A cikin rahotonsa, shugaban bankin, Mista Hamid Joda, ya bayyana cewa harkokin kudade a 2022 yana da matukar muhimmi ga ci gaba a cikin tafiyar masu ba da bashi babu ruwa duk da irin kalubalen da aka samu na nuna yanayin aiki, amma an samu nasarar cimma abubuwa masu yawa.

Dangane da harkokin kudade na bankin a cikin 2022, Joda ya ruwaito cewa Bankin TAJ ya samu karuwa a cikin muhimman abubuwa a shekarar, yayin da ma’auni ya karu da sama da 93 daga Naira biliyan 110 da aka samu na 2021 zuwa Naira biliyan 212, yayin da riba kafin fitar da haraji ya karu daga Naira biliyan 1.6 a 2021 zuwa Naira biliyan 5.081 biliyan a shekarar kudi ta 2022.

Ya kuma shaida wa masu hannun jarin cewa ribar da bankin ke samu a kowanne kaso ya karu da kashi 138 zuwa Naira 31.27 a 2022, idan aka kwatanta da Naira 13.11 da aka samu a shekarar 2021.

Game da shirye-shiryen kara bunkasa harkokin bankin nan da shekaru masu zuwa kuwa, Joda ya ce, “A kokarin da muke yi na inganta kayayyakin da ake samu ribar da babu ruwa da kuma tsarin hada-hadar banki a duk fadin kasar nan, hukumar gudanarwar ta Bankin TAJ sun kafa muhimman manufofi da za a bi a shekarar 2023.

“Muna shirin bude rassa da ofisoshin kasuwanci 110 a fadin manyan biranen jihohi da manyan cibiyoyin kasuwanci kafin shekarar 2024 da kuma bayar da kayayyaki da ayyuka na banki da babu ruwa ga kasuwanni, domin habaka hanyar sadarwar hukumarmu zuwa wakilai masu aiki 100,000 nan da 2025, don rage matsalolin harkokin kudi tare da habaka abokanan kasuwanci zuwa akalla miliyan hudu nan da 2027, saboda cimma bukatar mafi karancin gamsuwar abokin ciniki na kashi 85,” in ji shi.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan taron, kwararre kan harkokin kudi, Alhaji Tata Shekaru Omar, ya yaba wa hukumar gudanarwa bisa sabbin tsare-tsare da suka sanya har Bankin TAJ ya zama na sahun gaba a harkokin hada-hadar kudi na kasar nan.

Ya ce, “Bankin TAJ bai cika shekara hudu da kafawa ba, amma ya samu gagarumar riba a shekararsa ta farko da ya fara aiki, labari ne mai dadi da farin ciki ga duk masu hannun jari a bankin. Ina so in yi godiya ga shugaban bankin da daukacin tawagarsa da suka yi irin wannan aiki, musamman yadda bankin ke ba da riba ga masu hannun jari.”

TAJ
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama

Sabon Kwanturolan NIS Na Jihar Legas Ya Karɓi Ragama

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.