• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da Rashin Katabus Na Kananan Hukumomi Ke Yi Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Barazanar Da Rashin Katabus Na Kananan Hukumomi Ke Yi Ga Dimokuradiyyar Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rushewar shugabanci da tsari a matakin kananan hukumomi babbar barazana ce ga dimokuradiyyar Nijeriya, wanda ke janyo alamun tambayoyi a wurin masana shari’a da kungiyoyin al’umma game da tabbacin dimokuradiyyar Nijeriya.

Rikicin siyasar da ke gudana tsakanin Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara da wani bangaren majalisar dokokin jihar kan wa’adin shugabannin kananan hukumomi, ya fallasa yadda kusan dukkanin jihohin suka shiga ruguza tsarin shugabancin kananan hukumomi, inda zaben kananan hukumomi ya dogara da yadda gwamnoni suke so maimakon bin tsarin doka.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Mutane 75,000 Sun Kamu Da HIV, 45,000 Sun Rasu A Shekarar 2023 – NACA DG

A zantawarsu da Jaridar LEADERSHIP, kwararru a fannin tsaro sun goyi bayan wani furucin da babban hafsan sojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya yi a baya-bayan nan na cewa rashin tsaro da ake fama da shi a yawancin sassan kasar nan, usamman arewacin Nijeriya na da nasaba da rashin gudanar da mulki yadda ya kamata a kananan hukumomi.

Masu ruwa da tsaki da suka zanta da LEADERSHIP sun bayyana cewa cin hanci da rashawa da mamaye siyasa a matsayin babban abin da ke kara tunzura gwamnonin yin watsi da kundin tsarin mulkin kasar, sannan sun ce hukuncin kotun koli zai kawo karshen danniyar da gwamnoni suke yi wa kudaden kananan hukumomi.

A halin da ake ciki a yanzu, akwai makudan nairori na kananan hukumomi.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Tsakanin Janairu zuwa Mayu 2024, dukkan matakan gwamnati uku sun raba naira tiriliyan 5.759 daga asusun tarayya. Kananan Hukumomi 774 sun samu naira tiriliyan 1.416 kan wannan adadi.

LEADERSHIP ta yi kiyasin cewa kananan hukumomi 774 za su iya samun kudaden da suka kai naira tiriliyan 3.39 a 2024.

A watan Janairun 2024, kananan hukumomin sun samu naira biliyan 288.928, sun kuma samu naira biliyan 278.041 a watan Fabrairu, naira biliyan 267.153 a watan Maris, naira biliyan 288.688 a watan Afrilu da kuma naira biliyan 293.816 a watan Mayu.

Bincike da ra’ayoyin masana da LEADERSHIP ta samo ya nuna cewa rashin bai wa kananan hukumomi ‘yanci na gurgunta mulkin dimokuradiyya da rura wutar rashin tsaro da haifar da cin hanci da rashawa da ta da zaune tsaye tsakanin gwamnatocin jihohi da sauran jama’a a bangare guda, sannan ana samun rudani a tsakanin gwamnatocin jihohi da gwamnatin tarayya.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa kusan dukkanin gwamnonin jihohin da ke kan mulki sun nada mukaman rikon kwarya ta hanyar karya dokokin Nijeriya da kuma saba wa hukuncin kotun koli. Kamar gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya kai ga korar zababbun shugabannin kananan hukumomi.

Sai dai Jihar Anambra ta cire tuta wajen rashin bin doka kamar yadda wakilinmu ya ruwaito cewa an gudanar da zaben kananan hukumomi a shekarar 2014, shekaru goma da suka gabata.

A Jihar Ribas kuwa, an gudanar da muhawara kan wannan kuskure, inda wa’adin shugabannin kananan hukumomin da aka zaba ya kare a ranar 17 ga watan Yunin 2024.

Nan take gwamnan ya maye gurbinsu da masu rikon kwarya, yayin da majalisar jihar ta dage cewa ta tsawaita wa’adinsu ta hanyar wata doka mai cike da rudani.

Jihohin da suka gudanar da zaben kananan hukumomi a cikin shekaru uku da suka gabata sun hada da Sakkwato, Kaduna, Filato, Yobe, Ebonyi, Inugu, Kebbi, Neja, Adamawa, Oyo, Katsina, Ekiti, Borno, Gombe da Edo.

A watan Yulin 2021 ne Legas ta gudanar da zaben kananan hukumomi, amma ba ta shirin gudanar da wani zaben a 2025, wanda ya zarce shekaru uku da doka ta tanada.

A wasu jihohin kuma, an gudanar da zaben kananan hukumomi a Jihar Kwara a shekarar 2017, an gudanar a 2018 a Jihar Imo, a watan Disamba 2020 an gudanar a Jihar Kogi, a watan Oktoba 2020 an yi a Akwa Ibom, a watan Mayu 2020 an gudanar a Jihar Kusu Ribas, a watan Yuni 2021 an yi a Jihar Jigawa.

Jihar Bauchi ta gudanar da zaben kananan hukumomi a watan Oktoba na shekarar 2020. A Jihar Abiya ma an yi zaben a shekarar 2020, yayin da a Jihar Delta ya gudana a watan Maris na 2021.

Yayin da gwamnatin tarayya take kokarin dawo da tsarin mulki da cin gashin kai ga kananan hukumomi, wasu masa harkokin shari’a sun nuna rashin amincewa da tsarin.

Manyan lauyoyi da dama na Nijeriya sun yi ce-ce-ku-ce kan karar da gwamnatin tarayya ta shigar kan jihohi 36 na tarayyar kasar na neman cin gashin kan kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF) kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi, SAN, ya maka gwamnatocin jihohi a gaban kotun koli kan yadda gwamnonin jihohin ke rike kananan hukumomin ba bisa ka’ida ba.

Karar na neman cikakken ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomi a matsayin mataki na uku na gwamnati a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DimokuraÉ—iyyaKananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Next Post

Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Katabus
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.