ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da Rashin Katabus Na Kananan Hukumomi Ke Yi Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Katabus

Rushewar shugabanci da tsari a matakin kananan hukumomi babbar barazana ce ga dimokuradiyyar Nijeriya, wanda ke janyo alamun tambayoyi a wurin masana shari’a da kungiyoyin al’umma game da tabbacin dimokuradiyyar Nijeriya.

Rikicin siyasar da ke gudana tsakanin Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara da wani bangaren majalisar dokokin jihar kan wa’adin shugabannin kananan hukumomi, ya fallasa yadda kusan dukkanin jihohin suka shiga ruguza tsarin shugabancin kananan hukumomi, inda zaben kananan hukumomi ya dogara da yadda gwamnoni suke so maimakon bin tsarin doka.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Mutane 75,000 Sun Kamu Da HIV, 45,000 Sun Rasu A Shekarar 2023 – NACA DG

A zantawarsu da Jaridar LEADERSHIP, kwararru a fannin tsaro sun goyi bayan wani furucin da babban hafsan sojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya yi a baya-bayan nan na cewa rashin tsaro da ake fama da shi a yawancin sassan kasar nan, usamman arewacin Nijeriya na da nasaba da rashin gudanar da mulki yadda ya kamata a kananan hukumomi.

ADVERTISEMENT

Masu ruwa da tsaki da suka zanta da LEADERSHIP sun bayyana cewa cin hanci da rashawa da mamaye siyasa a matsayin babban abin da ke kara tunzura gwamnonin yin watsi da kundin tsarin mulkin kasar, sannan sun ce hukuncin kotun koli zai kawo karshen danniyar da gwamnoni suke yi wa kudaden kananan hukumomi.

A halin da ake ciki a yanzu, akwai makudan nairori na kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Tsakanin Janairu zuwa Mayu 2024, dukkan matakan gwamnati uku sun raba naira tiriliyan 5.759 daga asusun tarayya. Kananan Hukumomi 774 sun samu naira tiriliyan 1.416 kan wannan adadi.

LEADERSHIP ta yi kiyasin cewa kananan hukumomi 774 za su iya samun kudaden da suka kai naira tiriliyan 3.39 a 2024.

A watan Janairun 2024, kananan hukumomin sun samu naira biliyan 288.928, sun kuma samu naira biliyan 278.041 a watan Fabrairu, naira biliyan 267.153 a watan Maris, naira biliyan 288.688 a watan Afrilu da kuma naira biliyan 293.816 a watan Mayu.

Bincike da ra’ayoyin masana da LEADERSHIP ta samo ya nuna cewa rashin bai wa kananan hukumomi ‘yanci na gurgunta mulkin dimokuradiyya da rura wutar rashin tsaro da haifar da cin hanci da rashawa da ta da zaune tsaye tsakanin gwamnatocin jihohi da sauran jama’a a bangare guda, sannan ana samun rudani a tsakanin gwamnatocin jihohi da gwamnatin tarayya.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa kusan dukkanin gwamnonin jihohin da ke kan mulki sun nada mukaman rikon kwarya ta hanyar karya dokokin Nijeriya da kuma saba wa hukuncin kotun koli. Kamar gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya kai ga korar zababbun shugabannin kananan hukumomi.

Sai dai Jihar Anambra ta cire tuta wajen rashin bin doka kamar yadda wakilinmu ya ruwaito cewa an gudanar da zaben kananan hukumomi a shekarar 2014, shekaru goma da suka gabata.

A Jihar Ribas kuwa, an gudanar da muhawara kan wannan kuskure, inda wa’adin shugabannin kananan hukumomin da aka zaba ya kare a ranar 17 ga watan Yunin 2024.

Nan take gwamnan ya maye gurbinsu da masu rikon kwarya, yayin da majalisar jihar ta dage cewa ta tsawaita wa’adinsu ta hanyar wata doka mai cike da rudani.

Jihohin da suka gudanar da zaben kananan hukumomi a cikin shekaru uku da suka gabata sun hada da Sakkwato, Kaduna, Filato, Yobe, Ebonyi, Inugu, Kebbi, Neja, Adamawa, Oyo, Katsina, Ekiti, Borno, Gombe da Edo.

A watan Yulin 2021 ne Legas ta gudanar da zaben kananan hukumomi, amma ba ta shirin gudanar da wani zaben a 2025, wanda ya zarce shekaru uku da doka ta tanada.

A wasu jihohin kuma, an gudanar da zaben kananan hukumomi a Jihar Kwara a shekarar 2017, an gudanar a 2018 a Jihar Imo, a watan Disamba 2020 an gudanar a Jihar Kogi, a watan Oktoba 2020 an yi a Akwa Ibom, a watan Mayu 2020 an gudanar a Jihar Kusu Ribas, a watan Yuni 2021 an yi a Jihar Jigawa.

Jihar Bauchi ta gudanar da zaben kananan hukumomi a watan Oktoba na shekarar 2020. A Jihar Abiya ma an yi zaben a shekarar 2020, yayin da a Jihar Delta ya gudana a watan Maris na 2021.

Yayin da gwamnatin tarayya take kokarin dawo da tsarin mulki da cin gashin kai ga kananan hukumomi, wasu masa harkokin shari’a sun nuna rashin amincewa da tsarin.

Manyan lauyoyi da dama na Nijeriya sun yi ce-ce-ku-ce kan karar da gwamnatin tarayya ta shigar kan jihohi 36 na tarayyar kasar na neman cin gashin kan kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF) kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi, SAN, ya maka gwamnatocin jihohi a gaban kotun koli kan yadda gwamnonin jihohin ke rike kananan hukumomin ba bisa ka’ida ba.

Karar na neman cikakken ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomi a matsayin mataki na uku na gwamnati a kasar nan.

Katabus
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.