• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da ‘Yan Jarida Ke Fuskanta A Bakin Aiki

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayinmu
0
Barazanar Da ‘Yan Jarida Ke Fuskanta A Bakin Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da Nijeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya domin yin bikin zagayowar ranar kawo karshen cin zarfin da ake yi wa ‘yan jarida, ana ci gaba da ankarar da al’umma kan gudunmawar da ‘yan jarida ke bayar wa wajen wanzar da tsarin mulkin dimokiradiyya.

 

Tabbas, cin gashin kowane irin mulikin dimokiradiyya, ya danganta ne, da goyon bayan da kwararrun ‘yan jarida ke bayar wa, musamman ma ta hanyar damar da kafafen yada labarai ke bai wa al’umma su fadi ra’ayoyinsu, ta hanyar fadakarwa, ilimantawa, wanda hakan zai bayar da damar, yin muhawara a kan wani batu, da ya shafi kasa baki daya.

  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Karbo Bashin Dala 2.2bn Don Bunkasa Tattalin Arziki

A cewar hukumar kula da ilimi da al’adu da kimiyya ta majalisar dinkin duniya wato UNESCO, ta yi nuni da cewa, kawo karshen cin zarafin ‘yan jarida, wani abu ne, da babban kalubale da ake fuskanta a ‘yan kwanukan baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

Wannan jaridar, tana sane da yadda ‘yan jarida da kafafen yada labarai ke shiga cikin hadari, a yayin da suke kan gudanar da ayyukansu, musamman ma yadda ake azabtar da su, garkame su a gidan Yari ba bisa ka’ida ba, sace su, ciki har da hallaka su, saboda kawai sun wallafa labarai wadanda suka tabbatar da cewa, sahihai ne.

 

Irin wannan hatsarin da ‘yan jaridar kasar ke tsintar kansu a ciki ne, ya sanya wasu masu ruwa da tsaki, ciki har da kungiyoyin da ke ta fafutukar kare ‘yancin ‘yan Adam, suka bukaci gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu, da ta lalubo da mafita a kan hare-haren da ake kai wa a kan ‘yan jarida da suke gudanar da ayyukansu a fadin kasar.

 

A kiran da suka yi karo na biyu wanda yake kunshe a cikin sanarwar da suka fitar, Cibiyar bunkasa aikin jarida CJID, CG, gamayyar kungiyoyin ‘yan jarida 85 da kuma wasu masu kishin kasa da wasu kwararrun ‘yan jarida, sun bukaci da a gaggauta kawo karshen yawan kai wa ‘yan jarida hare-hare da cin zarafinsu a daukacin fadin Nijeriya.

 

Sai dai, daga shekarar 2017 zuwa gaba, hukumar UNESCO ta ce, an samu raguwar kisan da ake yiwa ‘yan jarida a yankunan da tashe-tsahen hankula suka auku.

 

UNESCO a wata bibiyar bayanai da ta gudanar a 2023, ta ce, sama da ‘yan jarida 50 ne aka hallaka, a yankunna da aka samu tashe-tashen hankula, wanda hakan ya karu a zangon farko na shekarar 2024.

 

Daga shekarun 2006 zuwa 2024, sama da ‘yan jarida 1,700 ne aka kashe a fadin duniya, wadanda kuma kusan kashi tara ne, daga cikin goma, da suka yi saura, a bangaren Shari’a an gaza warware maganar.

 

Bisa kididdigar Cibiyar CJID kan harin da aka kai wa ‘yan jarida a Nijeriya, sun kai 51.

 

CJID ta ce, bisa nazarin da ta yi ta ce, kashi 37 na aukuwar wadannan lamurran sun faru ne daga ranar 1 zuwa ranar 30 na watan Yunin shekarar 2024, wanda hakan ya nuna karuwar lamarin ne.

 

Kazalika ma, tun bayan wasikar farko ta kai harin a kan ‘yan jarida da CJID ta aika, Cibiyar ta tattara adadin hare-hare a kan ‘yan jarida da ta tabbar sun kai 90 daga ranar 1 na watan Yuli zuwa ranar 22 ga watan Oktobar 2024.

 

A bangaren alkalumman Cibiyar kare ‘yan jarida ta kasa da kasa kuwa wato Press IPC ta ce, sama da ‘yan jarida 40 aka kai wa hare-hare a Nijeriya a cikin watan tara na shekarar 2024.

 

Hukumar ta UNESCO ta lura da cewa, hare-haren da aka kai wa ‘yan jarida a Nijeriya na ci gaba da jefa fargaba ga kafafen yada labarai, musamman ma wajen gudanar da ayyukansu.

 

Kazalika ma, ci gaba da take ‘yancin ‘yan jarida a Nijeiya da wasu masu ruwa da tsaki ke yi, hakan na kara haifar da tararrabi kan kariyar da ta kamata su samu wanda hakan kuma ke zamowa wata barazanar da mulkin dimokiradiyya da samun damar fadar ra’ayi.

 

Bugu da kari kuma, wannan jaridar ta goyi bayan yunkurin da wadannan kungiyoyin kan kiraye-kirayen da suka yiwa gwamnatin tarayya na ta wanzar da dokoki da kuma daukar matakan bai wa ‘yan jarida kariya da kuma gudanar da aikinsu, ba tare da jin wani tsoro ba, ko fargaba ko kai masu hare-hare ba.

 

Wannan ya hada da gudanar da zurzurfan gudanar da bincike kan garkame ‘yan jarida da hare-haren da aka kai masu, sannan kuma a tabbatar da duk wadanda suka aikata masu wannan ta’asar, an tuhume su da hukuntawa.

 

Bugu da kari ma, akwai kuma bukatar a tilastawa bangaren gwamnati domin ta rinka mutunta ‘yancin ‘yan jarida da ba su kariya kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya, ya tanadar.

 

Hakanan ma da, akwai bukatar kafafaen yada labarai su tattauna da jami’an tsaro, musamman ma sojoji, ‘yan sanda, DSS, kan gudunmawar da za su bada ta kare rayukan ‘yan jarida.

 

Akwai bukatar shugaban kasa Tinubu, ya bayar da umarni kan korafe-korafen a kan jarida domin hukumar da ke karbar korafe-korafen cin zarafin ‘yan jarida da (NMCC), ta gudanar da bincike.

 

Yin hakan ya zama wajibi ne, musamman domin a tabbatar da ana gudanar da shugabanci nagari da kuma isar da bayanai ga ‘yan kasar.

 

A ranar 2 ga watan Nuwamba ne, Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniya ya ware, a matsayin ranar cin zarafin ‘yan jarida ta duniya wadda ta ke da matsya mai lambar A/RES/68/163.

 

An dai zabo ranar ta biyo bayan kisan gillar da aka yiwa ‘yan jarida biyu ‘yan kasar Faransa a kasar Mali ranar 2 ga watan Nuwamba 2013.

 

Bikin ranar ta duniya ya bana, ya guda ne, daga ranar 6 zuwa 7 na Nuwambar 2024 a shalkwatar tarayyar Afirka AU da ke a babban birnin Addis Ababa, na kasar Ethiopia.

 

Taken bikin na bana shi ne, ‘bai wa ‘’yan jarida kariyar gaggawa a yayin dauko rahotanni a yankunan da ake yin rikice-rikice’’.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Koka Kan Yawaitar Satar Magani A Asibiti

Next Post

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Haura Dala Biliyan 42.9 – Rahoto

Related

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

5 days ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

2 weeks ago
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

2 months ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

2 months ago
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Ra'ayinmu

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

3 months ago
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
Ra'ayinmu

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

3 months ago
Next Post
Yan jarida

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Haura Dala Biliyan 42.9 – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.