ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da ‘Yan Jarida Ke Fuskanta A Bakin Aiki

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Yan jarida

A yayin da Nijeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya domin yin bikin zagayowar ranar kawo karshen cin zarfin da ake yi wa ‘yan jarida, ana ci gaba da ankarar da al’umma kan gudunmawar da ‘yan jarida ke bayar wa wajen wanzar da tsarin mulkin dimokiradiyya.

 

Tabbas, cin gashin kowane irin mulikin dimokiradiyya, ya danganta ne, da goyon bayan da kwararrun ‘yan jarida ke bayar wa, musamman ma ta hanyar damar da kafafen yada labarai ke bai wa al’umma su fadi ra’ayoyinsu, ta hanyar fadakarwa, ilimantawa, wanda hakan zai bayar da damar, yin muhawara a kan wani batu, da ya shafi kasa baki daya.

ADVERTISEMENT
  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Karbo Bashin Dala 2.2bn Don Bunkasa Tattalin Arziki

A cewar hukumar kula da ilimi da al’adu da kimiyya ta majalisar dinkin duniya wato UNESCO, ta yi nuni da cewa, kawo karshen cin zarafin ‘yan jarida, wani abu ne, da babban kalubale da ake fuskanta a ‘yan kwanukan baya.

 

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Wannan jaridar, tana sane da yadda ‘yan jarida da kafafen yada labarai ke shiga cikin hadari, a yayin da suke kan gudanar da ayyukansu, musamman ma yadda ake azabtar da su, garkame su a gidan Yari ba bisa ka’ida ba, sace su, ciki har da hallaka su, saboda kawai sun wallafa labarai wadanda suka tabbatar da cewa, sahihai ne.

 

Irin wannan hatsarin da ‘yan jaridar kasar ke tsintar kansu a ciki ne, ya sanya wasu masu ruwa da tsaki, ciki har da kungiyoyin da ke ta fafutukar kare ‘yancin ‘yan Adam, suka bukaci gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu, da ta lalubo da mafita a kan hare-haren da ake kai wa a kan ‘yan jarida da suke gudanar da ayyukansu a fadin kasar.

 

A kiran da suka yi karo na biyu wanda yake kunshe a cikin sanarwar da suka fitar, Cibiyar bunkasa aikin jarida CJID, CG, gamayyar kungiyoyin ‘yan jarida 85 da kuma wasu masu kishin kasa da wasu kwararrun ‘yan jarida, sun bukaci da a gaggauta kawo karshen yawan kai wa ‘yan jarida hare-hare da cin zarafinsu a daukacin fadin Nijeriya.

 

Sai dai, daga shekarar 2017 zuwa gaba, hukumar UNESCO ta ce, an samu raguwar kisan da ake yiwa ‘yan jarida a yankunan da tashe-tsahen hankula suka auku.

 

UNESCO a wata bibiyar bayanai da ta gudanar a 2023, ta ce, sama da ‘yan jarida 50 ne aka hallaka, a yankunna da aka samu tashe-tashen hankula, wanda hakan ya karu a zangon farko na shekarar 2024.

 

Daga shekarun 2006 zuwa 2024, sama da ‘yan jarida 1,700 ne aka kashe a fadin duniya, wadanda kuma kusan kashi tara ne, daga cikin goma, da suka yi saura, a bangaren Shari’a an gaza warware maganar.

 

Bisa kididdigar Cibiyar CJID kan harin da aka kai wa ‘yan jarida a Nijeriya, sun kai 51.

 

CJID ta ce, bisa nazarin da ta yi ta ce, kashi 37 na aukuwar wadannan lamurran sun faru ne daga ranar 1 zuwa ranar 30 na watan Yunin shekarar 2024, wanda hakan ya nuna karuwar lamarin ne.

 

Kazalika ma, tun bayan wasikar farko ta kai harin a kan ‘yan jarida da CJID ta aika, Cibiyar ta tattara adadin hare-hare a kan ‘yan jarida da ta tabbar sun kai 90 daga ranar 1 na watan Yuli zuwa ranar 22 ga watan Oktobar 2024.

 

A bangaren alkalumman Cibiyar kare ‘yan jarida ta kasa da kasa kuwa wato Press IPC ta ce, sama da ‘yan jarida 40 aka kai wa hare-hare a Nijeriya a cikin watan tara na shekarar 2024.

 

Hukumar ta UNESCO ta lura da cewa, hare-haren da aka kai wa ‘yan jarida a Nijeriya na ci gaba da jefa fargaba ga kafafen yada labarai, musamman ma wajen gudanar da ayyukansu.

 

Kazalika ma, ci gaba da take ‘yancin ‘yan jarida a Nijeiya da wasu masu ruwa da tsaki ke yi, hakan na kara haifar da tararrabi kan kariyar da ta kamata su samu wanda hakan kuma ke zamowa wata barazanar da mulkin dimokiradiyya da samun damar fadar ra’ayi.

 

Bugu da kari kuma, wannan jaridar ta goyi bayan yunkurin da wadannan kungiyoyin kan kiraye-kirayen da suka yiwa gwamnatin tarayya na ta wanzar da dokoki da kuma daukar matakan bai wa ‘yan jarida kariya da kuma gudanar da aikinsu, ba tare da jin wani tsoro ba, ko fargaba ko kai masu hare-hare ba.

 

Wannan ya hada da gudanar da zurzurfan gudanar da bincike kan garkame ‘yan jarida da hare-haren da aka kai masu, sannan kuma a tabbatar da duk wadanda suka aikata masu wannan ta’asar, an tuhume su da hukuntawa.

 

Bugu da kari ma, akwai kuma bukatar a tilastawa bangaren gwamnati domin ta rinka mutunta ‘yancin ‘yan jarida da ba su kariya kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya, ya tanadar.

 

Hakanan ma da, akwai bukatar kafafaen yada labarai su tattauna da jami’an tsaro, musamman ma sojoji, ‘yan sanda, DSS, kan gudunmawar da za su bada ta kare rayukan ‘yan jarida.

 

Akwai bukatar shugaban kasa Tinubu, ya bayar da umarni kan korafe-korafen a kan jarida domin hukumar da ke karbar korafe-korafen cin zarafin ‘yan jarida da (NMCC), ta gudanar da bincike.

 

Yin hakan ya zama wajibi ne, musamman domin a tabbatar da ana gudanar da shugabanci nagari da kuma isar da bayanai ga ‘yan kasar.

 

A ranar 2 ga watan Nuwamba ne, Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniya ya ware, a matsayin ranar cin zarafin ‘yan jarida ta duniya wadda ta ke da matsya mai lambar A/RES/68/163.

 

An dai zabo ranar ta biyo bayan kisan gillar da aka yiwa ‘yan jarida biyu ‘yan kasar Faransa a kasar Mali ranar 2 ga watan Nuwamba 2013.

 

Bikin ranar ta duniya ya bana, ya guda ne, daga ranar 6 zuwa 7 na Nuwambar 2024 a shalkwatar tarayyar Afirka AU da ke a babban birnin Addis Ababa, na kasar Ethiopia.

 

Taken bikin na bana shi ne, ‘bai wa ‘’yan jarida kariyar gaggawa a yayin dauko rahotanni a yankunan da ake yin rikice-rikice’’.

Yan jarida
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
Yan jarida
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • Sulaiman
    An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Yan jarida

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Haura Dala Biliyan 42.9 – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.