• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barkewar Kwalara: Ya Kamata A Dakatar Da Yin Kunu Da Zobo – Karamin Ministan Muhalli

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Kwalara

Sakamakon barkewar cutar kwalara a wasu sassan Nijeriya, gwamnatin tarayya ta bukaci ‘yan Nijeriya su guji hada kunu da zobo da kuma fura domin takaita barkewar cutar.

Karamin ministan muhalli, Iziak Salako shi ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja.

  • Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya
  • Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)

Salako ya yi kira ga ‘yan Nijeriya su dauki matakan kariya kamar irinsu tsaftace muhalli a ko da yaushe da zubar da sahara a wuraren da ya kamata.

“Ko tabbatar da tsaftace ruwan da suke sha. Ruwa na daya daga cikin musabbabin barkewar cutar, ya kamata a dunga tafasa ruwan da ake amfani da shi a cikin gidaje.

“Ya kamata mutane su daina hada kayayyakin sha kamar irinsu kunu, zobo, nono, koko da sauran abubuwan sha sai dai idan har an dauki matakan kariya ta yadda ba za a kamu da cutar ba.

LABARAI MASU NASABA

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

“A dunga wanke hannu da sabulu a ko da yaushe a cikin ruwan da ake wucewa, musamman bayan an fito daga bayi, a dunga wanke yara idan suka shiga bayi kafin su ci abinci da kuma bayan sun ci abinci da kuma lokacin da suka yi wasa da dabobi,” in ji shi.

Haka kuma ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da na kananan hukumomi su kara kulawa da tsaftar muhalli a wurarin sayar da abinci da abubuwan sha da ke fadin kasar nan.

Wadannan wurare sun hada da kasuwanni, gareji, makarangtu, wuraren sayar da abinci, cibiyoyin wasanni, wuraren ibada da kuma sauran wurare da jama’a suke haduwa su ji abinci.

Salako ya ce daukan matakan kariya zai taimaka wajen dakile yaduwar cutar kwalara da kuma samun damar kulawa da cutar. Ya kuma bukaci kwamishinonin muhalli da shugabannin kananan hukumomi su tallafa wa jami’an kula da tsaftar muhalli wajen tsaftace muhallin al’umma.

Ya kuma bukaci samun goyon bayan hukumomin kiwon lafiya da sauran masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da matakan da gwamnatin tarayya ta dauka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya
Manyan Labarai

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Next Post
An Shiga Alhini A Nijar Bayan Harin ‘Yan Bindiga Ya Hallaka Sojoji 20

An Shiga Alhini A Nijar Bayan Harin 'Yan Bindiga Ya Hallaka Sojoji 20

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025
Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

October 24, 2025
Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

October 24, 2025
Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.