Alhaji Naziru Tijjani Idris da aka fi sani da Naziru Annatija da ke harkokin saye da sayar da gidaje da filaye a unguwar Rimin Zakara, ya bayyana cewa batun sanya jan fenti da ma’aikatar kasa ta Jihar Kano ta yi kwanakin baya ga mazauna unguwar Rimin Zakara da ke cikin karamar hukumar Unggo a Jihar Kano, wanda ya ta tayar da hankulan al’ummar yankin, inda suke ganin wata kila za a rushe masu gidajen da suka mallaka shekara da shekaru, to ba gaskiya ba ne.
Ya bayyana hakan ne da yake zantawa da manema labarai, Alhaji Naziru ya ce idan gwamnati za ta rushe gidaje ba wannan hanya take bi ba, sanya fentin na kidayan gidaje ne, amma ya tabbatar da cewa duk abin da gwamnatin za ta yi a unguwar, za ta yi adalci ba za ta yi san ranta ba, domin gwamnati ce mai sauraren al’umma.
- Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba
- Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
Ya yi kira ga mazauna unguwar dama masu niyar zuwa sayen gida ko fili da su kwantar da hankulansu, batun rushe gidaje ba gaskiya ba ne.
Shi ma da yake nasa jawabin ga manema labarai, Alhaji Ishak Abba Madabo da aka fi sani da Shawus, ya ce gwamnatin Abba Kabir Yusuf, ba za ta yi abin da zai cutar da al’ummar unguwar ba, saboda haka ya yi kira ga wadanda suke da gidaje ko fili da su kwantar da hankulansu.
Shawus, ya taya al’ummar Musulmin jihar murnar kammala bikin sallah lafiya da fatan Allah ya dawo mana da alhazanmu gida lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp