• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
in Manyan Labarai
0
Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata tawagar haɗin gwuiwa daga jihohin Bauchi da Gombe ta nuna damuwa matuƙa kan jinkirin da ake samu a aikin ci gaban haƙar mai na Kolmani, wani babban shiri da aka fara a kan iyakar jihohin biyu.

Tawagar wadda ta ƙunshi Kwamishinan Raya Albarkatun Ƙasa na Jihar Bauchi, Muhammad Maiwada Bello, da Kwamishinan Ma’aikatar Albarkatun Ƙasa na Jihar Gombe, Sunusi Ahmad Pindiga, sun bayyana matsayinsu ne yayin da suka kai ziyara ta musamman zuwa ramin haƙar man da ke Kolmani.

  • Kwamitin Ɗanyen Mai Ya Nuna Rashin Gamsuwa Da Jinkirin Haƙo Mai A Kolmani
  • Bayan Wata 16 Da Kaddamarwa: Gwamnati Ta Dakatar Da Hakar Man Kolmani

A yayin ziyarar, sun bayyana rashin jin daɗinsu kan yadda aikin ke tafiya a hankali, inda suka buƙaci kamfanin da ke da alhakin aikin da ya gabatar da cikakken bayani game da matsayin aikin da kuma lokacin da za a kammala.

Kwamishina Bello ya ce, “Wannan aiki yana da matuƙar muhimmanci ga tattalin arziƙin jihohinmu biyu. Jinkirin da ake samu yana rage wa al’umma burin da suke da shi. Dole ne mu shiga tsakani domin a gaggauta aiwatar da abubuwan da suka dace.”

Shi ma a nasa jawabin, Kwamishina Pindiga ya jaddada buƙatar bayyananniyar mu’amala da gaskiya daga masu aikin. “Wannan aikin tarihi ne ga yankin Arewa maso Gabas. Ba za mu amince a mayar da shi saniyar ware ba saboda rashin tsari ko sakacin aiki.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

Tawagar ta ƙunshi kwamishinoni, da sakatarorin dindindin, da daraktocin albarkatun man fetur da kuma manyan shugabannin gargajiya daga jihohin biyu, wanda hakan ya nuna muhimmancin aikin da kuma haɗin kan da ake nema domin ganin ya cimma nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiCrudeGombeKolmaniOil
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Cike Da Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari — Atiku

Next Post

Gwamna Abba Ya Yi Alhinin Rasuwar Muhammadu Buhari

Related

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

2 hours ago
An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata

6 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina

6 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Wani Gidan Bene Mai Hawa Uku Ya Rufto, Ya Kashe Mutum 4, Da Jikkata 7 A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: Wani Gidan Bene Mai Hawa Uku Ya Rufto, Ya Kashe Mutum 4, Da Jikkata 7 A Kano

7 hours ago
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi
Manyan Labarai

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

8 hours ago
Next Post
Gwamna Abba Ya Yi Alhinin Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamna Abba Ya Yi Alhinin Rasuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

July 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

July 14, 2025
Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

July 14, 2025
Gwamna Abba Ya Yi Alhinin Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamna Abba Ya Yi Alhinin Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani

Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani

July 14, 2025
Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

Ina Cike Da Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari — Atiku

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.