• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan karbar makudan kudade a matsayin kudin fansa, wani kasurgumin dan fashin nan mai suna Dogo Daji, ya saki hudu daga cikin dalibai 11 da suka yi garkuwa da su a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya da ke Yauri, Jihar Kebbi.

An tattaro cewa biyu daga cikin daliban da aka sako sun dawo da jarirai biyu a hannunsu.

  • Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe
  • Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

Dogo Daji ya jaddada cewa sai an cika wasu sharuda da gwamnatin Jihar Kebbi kafin a sako sauran ‘yan matan.

Majiyoyi sun kara da cewa dole ne iyaye da sauran masu ruwa da tsaki su samar da kudin fansa a lokacin da gwamnatin Jihar Kebbi ta ki biyan bukatun ‘yan bindigar.

Sai da iyayen daliban sun roki ‘yan Nijeriya da su kawo musu agajin kudi domin ceto ‘ya’yansu daga hannun wadanda suka sace su.

Labarai Masu Nasaba

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

A cikin wata wasika da ta aike wa daukacin ‘yan Nijeriya a watan Janairun 2023, wadda Leadership Hausa ta samu, kungiyar da aka fi sani da “Kwamitin Iyayen dalibai 11 da aka sace na F.G.C Birnin Yauri, Jihar Kebbi, Nijeriya,” ta bukaci taimakon kudi domin tara zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa da za a biya ‘yan ta’adda.

A cikin wasikar, shugaban kwamitin iyayen, Salim Ka’oje da kuma Mista Daniel Alkali, sun ce ‘ya’yansu mata sun kasance a hannun wadanda suka sace su kusan watanni 20 kawo yanzu.

“…Kuma wadanda suka sace ‘yan matan suna neman Naira miliyan 100 kafin su sako su,” in ji su.

Idan za a iya tunawa, an yi garkuwa da daliban mata 11 ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari makarantarsu a ranar 17 ga watan Yuni 2021.

A watan Nuwamban shekarar da ta gabata ne aka ruwaito cewa wasu daga cikin ‘yan matan sun haihu, yayin da wasu kimanin hudu ke dauke da juna biyu a lokacin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiDan BindigaGarkuwaKudin FansaKwalejin Yauri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Next Post

An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

Related

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

6 days ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 weeks ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

4 weeks ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

1 month ago
Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda
Da ɗumi-ɗuminsa

Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda

3 months ago
Umar Farouk Ibrahim (Sakataren Gwamnatin Kano)
Da ɗumi-ɗuminsa

Watanni 2 Da Sauke Baffa Bichi, An Nada Umar Farouk Mukamin Sakataren Gwamnatin Kano

3 months ago
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.