ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
'Yan Wasa

A satin daya gabata ne dan wasa Sadio Mane da Leroy Sane suka yi fada a dakin hutun ‘yan wasa, bayan tashi daga Champions League, kamar yadda wasu jaridu suka wallafa.

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ce ta doke Bayern Munich 3-0 a wasan farko zagayen kuarter finals a gasar zakarun Turai a Etihad kuma ‘yan wasan biyu sun bai wa hammata iska, bayan tashi daga karawar har sai da aka shiga tsakaninsu.

  • Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands
  • Me Ya Sa Karin Kamfanonin Ketare Suka Samu Ra’ayin Bai Daya Kan Zuwa Kasar Sin Don Raya Kansu?

Rahotanni sun bayyana cewa Mane ya naushi Sane tsohon dan kwallon Manchester City a fuska, har lebensa ya dan tsage sai dai ba wannan ne karon farko da aka yi fada tsakanin ‘yan kungiya daya ba, ko dai a wajen atisaye har a filin wasa ko bayan an kammala gasa.

ADVERTISEMENT

Tuni kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta dakatar da dan wasa Sadio Mane daga buga mata wasa ranar Asabar din da ta gabata, ta kuma ce za ta hukunta shi bisa abinda ya faru.

-Ga jerin wasu daga fadan da aka yi tsakanin ‘yan kungiya daya:-

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Ibrahimobic da Onyewu

Dan wasa Zlatan Ibrahimobic ya yi kaurin suna wajen fada da abokan wasansa, domin ya taba yi wa Rafael ban der Baart barazanar zai karya masa kafa a Ajad ya kuma naushi Jonathan Zebina a fuska a Jubentus.

To sai dai wanda ya fi muni shi ne wanda ya yi a kungiyar kwallon kafa ta AC Milan, inda ya yi fada da Oguchi Onyewu, wanda ke buga wasa aro a Newcastle United daga kungiyar Italiya.

Batty da Le Saud

Blackburn Robers ta kasa taka rawar gani a Champions League, bayan lashe Premier League a lokacin ta ziyarci Spartak Moscow a wasa na biyar a cikin rukuni, bayan kasa yin nasara a fafatawar biyar.

A Rashan an ci Blackburn 3-0 a wasan ne Dabid Batty da Graeme Le Saud suka dunga dukan juna da kyar aka raba su. Drinkwater da Jota Ba za ka taba cewa ‘yan wasan da suka yi zaman benci za su bai wa hammata iska ba, abin da ya faru tsakanin Drink Water da Jota kenan a wajen atisaye, kwana daya tsakani da Aston Billa ta ci Leicester City 4-0 – ‘yan wasan Leicester da ba su buga karawar ba na atisaye a Bodymoor Hearth – sai cece kuce ya barke tsakanin Drinkwater da Jota, inda ‘yan wasan Ingila suka yi wa kansu gware, sai da aka shiga tsakaninsu.

Lloris da Son Tottenham ta yi nasara a kan kungiyar kwallon Eberton da cin 1-0 a watan Yulin shekara ta 2020, amma batun da ya fi jan hankali bayan hutu shi ne rigima tsakanin Gugo Lloris da Son Heung-min.

Mai tsaron ragar Tottenham ya tuhumi Son da kin dawowa ya tare kwallo, daga baya suka barke da kokawa har sai da Giobani Lo Celso da Harry Winks suka shiga tsakani, da aka tashi daga wasan sun rungumi juna, sannan bayan tashi daga wasan kociyan kungiyar, Jose Mourinho ya ce abin da ya faru abin ban sha’awa ne.

Mitrobic da Kamara

Aleksandar Mitrobic da Aboubakar Kamara sun dambata a tsakaninsu, bayan da Kamara ya karbe kwallo daga hannun dan Serbia suna Fulham ya buga fenariti a karawa da Huddersfield – akuma bi ci ba.

Adebayor da Bendtner

Emmanuel Adebayor shima daya daga ‘yan wasan da ke fada da abokan wasansa ne, sun bai wa hammata iska da Kolo Toure a Manchester City a

lokacin atisaye a 2011 sai dai tun kafin wannan, Adebayo ya yi fada da Nicklas Bendtner a Arsenal a 2008, wanda aka ce ya yi wa dan kasar Denmark gware a wasan da Tottenham ta ci 5-1 a League Cup wasan daf da karshe.

Robben da Ribery

Za’a iya cewa abin mamaki idan aka ce an yi fada tsakanin Arjen Rubben da Frank Ribery a lokacin gasar zakarun turai na Champions League

tsakanin Bayern Munich da Real Madrid. ‘Yan wasan guda biyu sun yi takaddama kan wanda zai yi bugun tazara, an yi zargin Ribery ya naushi Robben, amma Bayern ba ta ce komai kan lamarin kuma har yanzu babu wata magana daga kungiyar.

Shearer da Gillespie

An yi wani kazamin rikici tsakanin Alan Shearer wanda ta kai sai da aka dangana da Keith Gillespie zuwa asibiti ‘yan wasan Newcastle United a kakar wasa ta shekarar 1997.

Lehmann da Amoroso

Daman dai an bayyana cewa Jens Lehmann ba shi da hakuri ko kadan, ya kuma kalubalanci Marcio Amoroso, bayan da kungiyar Schalke ta zura kwallo a kungiyar su Borussia Dortmund a 2003.

An bai wa mai tsaron raga Lehman jan kati a karawar, wanda ya zama mai tsaron raga na farko a Bundesliga mai wannan tarihin da aka kora karo na hudu – daga baya aka soke kwallon da cewar akwai satar gida – inda suka tashi canjaras.

Ljungberg da Mellberg Mare-mare aka yi tsakanin Freddie Ljungberg da Olof Mellberg, wanda hakan ya ja hankalin manema labarai a lokacin da ake shirin zuwa gasar kofin duniya a kasashen Korea da Japan a 2002.

Ricksen da Radimob

Rahotanni sun bayyana cewa Fernando Ricksen mafadaci ne, wanda ya yi rigima da kyaftin, Bladislab wata daya da komawarsa Zenit sai dai tun kafin nan ya yi rigima da Malaga a lokacin atisaye.

Za’a iya cewa fadan da aka yi tsakanin ‘yan kungiya daya a tarihi yana da yawa da aka yi a baya, za kuma a ci gaba da yi duk da matakan ladabtarwa da kungiyoyi ke dauka a kan ‘yan wasan.

'Yan Wasa
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.