ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

by Sadiq
3 years ago
Kudin Fansa

Bayan karbar makudan kudade a matsayin kudin fansa, wani kasurgumin dan fashin nan mai suna Dogo Daji, ya saki hudu daga cikin dalibai 11 da suka yi garkuwa da su a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya da ke Yauri, Jihar Kebbi.

An tattaro cewa biyu daga cikin daliban da aka sako sun dawo da jarirai biyu a hannunsu.

  • Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe
  • Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

Dogo Daji ya jaddada cewa sai an cika wasu sharuda da gwamnatin Jihar Kebbi kafin a sako sauran ‘yan matan.

ADVERTISEMENT

Majiyoyi sun kara da cewa dole ne iyaye da sauran masu ruwa da tsaki su samar da kudin fansa a lokacin da gwamnatin Jihar Kebbi ta ki biyan bukatun ‘yan bindigar.

Sai da iyayen daliban sun roki ‘yan Nijeriya da su kawo musu agajin kudi domin ceto ‘ya’yansu daga hannun wadanda suka sace su.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

A cikin wata wasika da ta aike wa daukacin ‘yan Nijeriya a watan Janairun 2023, wadda Leadership Hausa ta samu, kungiyar da aka fi sani da “Kwamitin Iyayen dalibai 11 da aka sace na F.G.C Birnin Yauri, Jihar Kebbi, Nijeriya,” ta bukaci taimakon kudi domin tara zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa da za a biya ‘yan ta’adda.

A cikin wasikar, shugaban kwamitin iyayen, Salim Ka’oje da kuma Mista Daniel Alkali, sun ce ‘ya’yansu mata sun kasance a hannun wadanda suka sace su kusan watanni 20 kawo yanzu.

“…Kuma wadanda suka sace ‘yan matan suna neman Naira miliyan 100 kafin su sako su,” in ji su.

Idan za a iya tunawa, an yi garkuwa da daliban mata 11 ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari makarantarsu a ranar 17 ga watan Yuni 2021.

A watan Nuwamban shekarar da ta gabata ne aka ruwaito cewa wasu daga cikin ‘yan matan sun haihu, yayin da wasu kimanin hudu ke dauke da juna biyu a lokacin.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.