ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

by Sadiq
3 years ago
Kudin Fansa

Bayan karbar makudan kudade a matsayin kudin fansa, wani kasurgumin dan fashin nan mai suna Dogo Daji, ya saki hudu daga cikin dalibai 11 da suka yi garkuwa da su a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya da ke Yauri, Jihar Kebbi.

An tattaro cewa biyu daga cikin daliban da aka sako sun dawo da jarirai biyu a hannunsu.

  • Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe
  • Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

Dogo Daji ya jaddada cewa sai an cika wasu sharuda da gwamnatin Jihar Kebbi kafin a sako sauran ‘yan matan.

ADVERTISEMENT

Majiyoyi sun kara da cewa dole ne iyaye da sauran masu ruwa da tsaki su samar da kudin fansa a lokacin da gwamnatin Jihar Kebbi ta ki biyan bukatun ‘yan bindigar.

Sai da iyayen daliban sun roki ‘yan Nijeriya da su kawo musu agajin kudi domin ceto ‘ya’yansu daga hannun wadanda suka sace su.

LABARAI MASU NASABA

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

Kotu Ta Ba Da Belin Sowore Kan N200m Tare Da Tsauraran Sharuɗa

A cikin wata wasika da ta aike wa daukacin ‘yan Nijeriya a watan Janairun 2023, wadda Leadership Hausa ta samu, kungiyar da aka fi sani da “Kwamitin Iyayen dalibai 11 da aka sace na F.G.C Birnin Yauri, Jihar Kebbi, Nijeriya,” ta bukaci taimakon kudi domin tara zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa da za a biya ‘yan ta’adda.

A cikin wasikar, shugaban kwamitin iyayen, Salim Ka’oje da kuma Mista Daniel Alkali, sun ce ‘ya’yansu mata sun kasance a hannun wadanda suka sace su kusan watanni 20 kawo yanzu.

“…Kuma wadanda suka sace ‘yan matan suna neman Naira miliyan 100 kafin su sako su,” in ji su.

Idan za a iya tunawa, an yi garkuwa da daliban mata 11 ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari makarantarsu a ranar 17 ga watan Yuni 2021.

A watan Nuwamban shekarar da ta gabata ne aka ruwaito cewa wasu daga cikin ‘yan matan sun haihu, yayin da wasu kimanin hudu ke dauke da juna biyu a lokacin.

MASU ALAKA

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

July 1, 2026
Kotu Ta Ba Da Belin Sowore Kan N200m Tare Da Tsauraran Sharuɗa
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Belin Sowore Kan N200m Tare Da Tsauraran Sharuɗa

June 30, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.