Jami’ar European American University ta buƙaci shahararren mawaƙin Hausa, Dauda Kahutu Rarara, tare da sauran mutanen da aka ce an karrama a Abuja, da su tuntuɓe ta domin a tantance cancantarsu na samun digirin girmamawa na haƙiƙa.
A cewar wata sanarwa da jami’ar ta wallafa a shafinta na yanar gizo, idan aka tabbatar da cancantarsu, za a karrama su da digirin a hukumance a taron yaye ɗalibai da za a gudanar a Nijeriya cikin watan Nuwamba, 2025. Jami’ar ta kuma nanata cewa ba za a karɓi ko sisi daga wurin kowa ba, domin kaucewa ayyukan ƴan damfara.
- Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU
- Na Fi Ɗaukar Noma A Matsayin Sana’a Fiye Da Waƙa -Rarara
Haka zalika, jami’ar ta bayyana cewa ta riga ta fara bincike kan waɗanda suka shirya taron da aka gudanar a Abuja a matsayin karramawa, wanda ta bayyana a matsayin “Damfara” da aka yi ba tare da saninta ba.
DLC Hausa ta rawaito cewa, sanarwar ta biyo bayan nesanta kanta da taron da ya gudana a ranar Asabar, inda aka ce an bai wa Rarara da wasu mutane digirin girmamawa, abin da jami’ar ta ce ƙarya ne gaba ɗaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp