ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fi Ɗaukar Noma A Matsayin Sana’a Fiye Da Waƙa -Rarara

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Rara

Shahararren mawakin siyasa a Nijeriya, Dauda Adamu Kahutu Rarara, ya yi karin haske dangane da yadda yake gudanar da rayuwarsa; a wata hira da aka yi da shi a kafar yada labarai ta DW Hausa. 

Mawakin, wanda ya shafe fiye da shekara 10 yana yin wakokin siyasa da na sarauta ya bayyana cewa; bayan harkar waka, yana kuma yin wasu sana’o’i da dama na yau da kullum.

  • Shirin “Rawar Yingge: Wakar Jarumai”
  • Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi

Tun da farko dai, mawakin ya bayyana yadda yake samun wasu lokuta na rayuwarsa, yana wasannin motsa jiki; domin samun karin lafiya. Rarara ya sake jaddada maganr cewa, shi dalibin ilimi ne na addinin musulunci, wanda ya yi karatu a gaban mahaifinsa da ya riga mu gidan gaskiya.

ADVERTISEMENT

Da yake amsa tambayoyi a kan ikirarin da wasu ke yi na cewa, sau da dama ya kan bijiro da wakoki a daidai lokacin da ake tsaka da shan wahala a Nijeriya, domin ya karkatar da hankalin mutane daga wahalar da ake ciki, sai ya buda baki ya ce; ko alama ba haka zancen yake ba, domin kuwa dukkanin wakokinsa yana yin su ne da dalili, idan ya yi waka; sai ta fado daidai gabar wani abu da yake faruwa a kasa, ba yana nufin yana yi ne; don kawar da hankulan mutane ba, in ji Rarara.

“Mutane da dama, na mayar da hankalinsu kan aibuna; maimakon abubuwan alhairan da nake yi, saboda haka; ko kadan ni ba na daukar wannan a matsayin komai face, hassada da wasu daga cikin mutane ke nuna min, amma idan kuma ka riga ka shiga gaban mutum, to fa babu wani abu da zai iya yi maka; wanda Allah Madaukakin Sarki, bai yi maka ba”, a cewar Rarara.

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Dauda ya kara da cewa, babu wata waka da zai yi ba tare da an bukaci ya yi ta don isar da wani sako ba. Haka zalika, Shugaba Tinubu, ba shi da wani buri na tara dukiya a halin yanzu; illa kawai dai fatan barin tarihi mai kyau a matsayinsa na Shugaban kasa, kamar yadda sauran mazan jiya; irin su Sir Ahmadu Bello da Abubakar Tafawa Balewa suka bari.

Dangane da abin da wasu ke dauka cewa, ana biyana makudan kudade; don yin wakokin da za su kawar da hankalin mutane, su sani cewa; na fi mayar da hankali a kan noma fiye da yadda nake yi wa harkar waka, dalili kuwa; ni manomi ne wanda a yanzu haka duk fadin yankin da nake, babu wani mai yin noma kamar ni.

Yanzu haka, ina noma a gona mai fadin Eka fiye da 100, sannan kuma; ina sa ran samun karin wata gonar mai girman Eka 500 da zan kara a kan wadda nake nomawa yanzu. Don haka, har Dam na sa aka yi min a cikin gonata, saboda noman rani; don haka kashi 70 na kudin shiga da nake samu yanzu, ya fito ne daga harkar noma, ba waka kamar yadda wasu ke tunani ba.

Daga karshe, mawakin ya ce; babu abin da yake jin dadi idan ya aikata, fiye da taimakon gajiyayyu, “Ina matukar jin dadi idan na taimaka wa wadanda ke bukatar taimako, domin abin da na yarda da shi shi ne, muddin ka taimaki wani; shi ma zai taimaki wani, daga karshe za a rasa wani wanda zai bukaci taimako a cikin mutane”, in ji Rarara.

Rara
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

MASU ALAKA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
Manyan Labarai

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027
Manyan Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Next Post
Dahuwar Kifi Ta Zamani

Dahuwar Kifi Ta Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.