• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Duk da naira biliyan 180 da tarayya ta bai wa jihohi don raba tallafin rage radadin kuncin rayuwa sakamakon cire tallafin mai, har yanzu ‘Yan Nijeriya na fama da kuncin rayuwa, bayan wata uku da bullo da shirin.

A ranar 17 ga wata Agusta 2023 gwamnatin tarayya ta sanar da raba wa jihohi 36 da babba birnin tarayya Abuja Naira biliyan 5 kowanne su amma shiru kake ji kamar an shuka dussa.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

Bayani ya nuna cewa, kashi 52 na kudaden an basu ne a matsayin tallafi yayin da sauran kashi 48 na naira biliyan 5 din za su biya a cikin wata 20.

Tallafin na naira biliyan 5 ana sa ran ya rage radadin da al’umma suke ji sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi. Amma maimakon a samu sauki, sai dai korafi daga al’umma kan tsarin rabon tallafin yayin da su kuma jihohin ke karewa.

Misali, a JIhar Neja duk da kwamitin rabo da gwamnatin jihar ta kafa tun daga kananan hukumomi don raba kayan da aka sayo na Naira Biliyan 5.23, wadanda suka samu tallafin sun ce an ba su mudu daya ne na shinkafa da kwayoyin taliya da indomi wanda kuma ba yadda zai iya maganin radadin da ake fuskanta na janye tallafin mai.

Labarin yana da dan dadi daga Jihar Borno, don an fara bayar da tallafin tun daga watan Yuli, inda aka raba wa gidaje fiye da 400,000 a fadin jihar, an kuma fi bayar da muhimmanci ne ga wadanda yakin Boko Haram ya shafa.

Shugaban kungiyar nakasassu ta Jihar Borno, Ahmadu Umar, ya ce, wasu daga cikin manbobinsa sun amfana da rabon tallafin.

“Bayan wannan, wasu mambobinmu 2,000 na karbar tallafin naira 15,000 a wata daga gwamnatin jihar,” in ji Umar.

Ko a ‘yan makonnin da suka gabata, LEADERSHIP Hausa ta ruwaito yadda tallafin ya yi karanci a Jihar Kano inda wasu suka yi korafi sosai a kan tsarin rabon tallafin wanda wasu ma suka ce ba su gani a kasa ba

Labarin daya ne daga jihohin Delta, Benue Ekiti, an fitar da makudan kudade an sayi kayayyaki amma kuma abin da ya bai ga hannun talakawa ba.

Haka nan a Jihar Imo inda wasu da suka amfana suka ce, an ba su shinkafa cikin robar fenti abin da ba zai isa ya ciyar da iyali daya mai mutun hudu ba, sun ce maimakon tallafin ya rage radadi sai kawai ya kara tashin hankali na talaucin da ake fama da shi a kasa.

A Akwa Ibom, tuni aka dakatar da rabon tallafin bayan da aka fara raba buhu 40 na shinkafa ga kauye daya an kuma raba wa kauyuka 2,272 a kananan hukumomi 31 na jihar.

A Jihohin Kuros Ribas da Ribas da sauransu, wadanda suka amfana daga tallafin da aka raba sun koka a kan karancinsa.

Wani magidanci mazaunin kauyen Emago da ke karamar hukumar Abua/Odual a Jihar Ribas, Ennator James, ya bayyana cewa, buhun shinkafa daya aka ba al’ummarsu inda ake da mutum fiye da 700, “domin kowa ya samu sai muka raba wa kowa kofi daya na shinkafar ga duk mutum daya,” in ji shi.

Shirin bayar da bashin Naira Biliyan 275 ga masu kananan masa’anantu bai fara aiki ba.

Bayani ya juna cewa, har zuwa wannan lokacin shirin bayar da bashin Naira Biliyan 275 masu kananan masana’anantu da gwamnnati ta sanar bai fara aiki ba.

A watan Agusta ne Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da a fitar da a fitar da Naira Biliyan 275 don bayar da bashi ga masu manya da kananan masa’anantu, ya ce an yi haka ne don karfafa manya da kanana masa’anantun ta yadda za su samar da ayuyukan yi ga al’umma Nijeriya.

Ya kuma kara da cewa, gamnatin tarayya za ta kashe naira Biliyan 75 a stakanin watan Yuli 2023 zua watan Maris na 2024.

An shirya cewa, kowanne kamfani zai iya samun bashin naira biliyan 1 za a kuma biya bashin ne a cikin wata 60.

Amma kuma majiyar gwamnati na cewa har zuwa yanzu hukumar kula harkokin masa’anantu (SMEDAN) suna can suna aikin tantance wadanda za su amfana daga wannan tallafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

9 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

9 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

10 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

10 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

12 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

13 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.