• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Duk da naira biliyan 180 da tarayya ta bai wa jihohi don raba tallafin rage radadin kuncin rayuwa sakamakon cire tallafin mai, har yanzu ‘Yan Nijeriya na fama da kuncin rayuwa, bayan wata uku da bullo da shirin.

A ranar 17 ga wata Agusta 2023 gwamnatin tarayya ta sanar da raba wa jihohi 36 da babba birnin tarayya Abuja Naira biliyan 5 kowanne su amma shiru kake ji kamar an shuka dussa.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

Bayani ya nuna cewa, kashi 52 na kudaden an basu ne a matsayin tallafi yayin da sauran kashi 48 na naira biliyan 5 din za su biya a cikin wata 20.

Tallafin na naira biliyan 5 ana sa ran ya rage radadin da al’umma suke ji sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi. Amma maimakon a samu sauki, sai dai korafi daga al’umma kan tsarin rabon tallafin yayin da su kuma jihohin ke karewa.

Misali, a JIhar Neja duk da kwamitin rabo da gwamnatin jihar ta kafa tun daga kananan hukumomi don raba kayan da aka sayo na Naira Biliyan 5.23, wadanda suka samu tallafin sun ce an ba su mudu daya ne na shinkafa da kwayoyin taliya da indomi wanda kuma ba yadda zai iya maganin radadin da ake fuskanta na janye tallafin mai.

Labarin yana da dan dadi daga Jihar Borno, don an fara bayar da tallafin tun daga watan Yuli, inda aka raba wa gidaje fiye da 400,000 a fadin jihar, an kuma fi bayar da muhimmanci ne ga wadanda yakin Boko Haram ya shafa.

Shugaban kungiyar nakasassu ta Jihar Borno, Ahmadu Umar, ya ce, wasu daga cikin manbobinsa sun amfana da rabon tallafin.

“Bayan wannan, wasu mambobinmu 2,000 na karbar tallafin naira 15,000 a wata daga gwamnatin jihar,” in ji Umar.

Ko a ‘yan makonnin da suka gabata, LEADERSHIP Hausa ta ruwaito yadda tallafin ya yi karanci a Jihar Kano inda wasu suka yi korafi sosai a kan tsarin rabon tallafin wanda wasu ma suka ce ba su gani a kasa ba

Labarin daya ne daga jihohin Delta, Benue Ekiti, an fitar da makudan kudade an sayi kayayyaki amma kuma abin da ya bai ga hannun talakawa ba.

Haka nan a Jihar Imo inda wasu da suka amfana suka ce, an ba su shinkafa cikin robar fenti abin da ba zai isa ya ciyar da iyali daya mai mutun hudu ba, sun ce maimakon tallafin ya rage radadi sai kawai ya kara tashin hankali na talaucin da ake fama da shi a kasa.

A Akwa Ibom, tuni aka dakatar da rabon tallafin bayan da aka fara raba buhu 40 na shinkafa ga kauye daya an kuma raba wa kauyuka 2,272 a kananan hukumomi 31 na jihar.

A Jihohin Kuros Ribas da Ribas da sauransu, wadanda suka amfana daga tallafin da aka raba sun koka a kan karancinsa.

Wani magidanci mazaunin kauyen Emago da ke karamar hukumar Abua/Odual a Jihar Ribas, Ennator James, ya bayyana cewa, buhun shinkafa daya aka ba al’ummarsu inda ake da mutum fiye da 700, “domin kowa ya samu sai muka raba wa kowa kofi daya na shinkafar ga duk mutum daya,” in ji shi.

Shirin bayar da bashin Naira Biliyan 275 ga masu kananan masa’anantu bai fara aiki ba.

Bayani ya juna cewa, har zuwa wannan lokacin shirin bayar da bashin Naira Biliyan 275 masu kananan masana’anantu da gwamnnati ta sanar bai fara aiki ba.

A watan Agusta ne Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da a fitar da a fitar da Naira Biliyan 275 don bayar da bashi ga masu manya da kananan masa’anantu, ya ce an yi haka ne don karfafa manya da kanana masa’anantun ta yadda za su samar da ayuyukan yi ga al’umma Nijeriya.

Ya kuma kara da cewa, gamnatin tarayya za ta kashe naira Biliyan 75 a stakanin watan Yuli 2023 zua watan Maris na 2024.

An shirya cewa, kowanne kamfani zai iya samun bashin naira biliyan 1 za a kuma biya bashin ne a cikin wata 60.

Amma kuma majiyar gwamnati na cewa har zuwa yanzu hukumar kula harkokin masa’anantu (SMEDAN) suna can suna aikin tantance wadanda za su amfana daga wannan tallafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

1 hour ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

2 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

3 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

8 hours ago
Kunci
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

9 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.