• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Laraba 20 ga watan nan na Disamba, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya zanta da takwaransa na Philippine Enrique A. Manalo ta wayar tarho.

A gabar da alakar Sin da Philippines ta shiga wani yanayi mai sarkakiya, don gane da batun tekun kudancin Sin, tattaunawar da manyan jami’an biyu suka yi ta tarho, ta janyo hankulan sassan kasa da kasa. Yayin zantawar, bangaren Sin ya fayyace cewa, Philippines ta sauya matsayar ta, ta janye daga alkawuran da ta dauka, tana kuma ci gaba da takalar rigima a yankin teku, wanda hakan keta halastattun hakkokin Sin ne da moriyar ta bisa doka.

  • Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Kyautata Yanayin Kasuwanci Da Kara Habaka Kasuwanni
  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Tun daga farkon wannan shekara, rahotanni na nuna yadda Philippines ta rika tura jiragen ruwan gwamnati, da na yaki, suna yin kutse a sassan ruwan dake daura da Ren’ai Jiao na tsibiran Nansha na kasar Sin, kana Philippines din ta rika aikewa da kayan gine gine zuwa ga jiragen dakon kaya na sojin ta da aka jibge ba bisa ka’ida ba, a wani mataki na wanzar da mamaya a yankin ruwan na Ren’ai Jiao.

Abun tambaya a nan shi ne, mene ne ya sa gwamnatin Philippine din aikata hakan? Masharhanta na ganin a daya bangaren, akwai murya mai karfi a Philippines dake ingiza batun tekun kudancin Sin, kuma shugaban Philippine na son amfani da hakan wajen karfafa karbuwarsa, ta hanyar nuna matsayin sa na rikau. A daya bangaren kuwa, yayin da hadin gwiwar Amurka da Philippines a fannin tsaro da sauran sassa ke kankama, manufofin waje na Philippines din sun fara karkara ga ra’ayoyin Amurka.

A fannin dangantakar Sin da Philippines, cikin shekarun baya bayan nan, Sin ta nuna halin dattaku, da hakuri wajen warware rashin fahimta game da batun tekun kudancin Sin tare da Philippines. To sai dai kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta sadaukar da wani hakkin mulkin yankunan ta. Tun farkon wannan shekara ta bana, Sin ta rika daukar jerin hakikanin matakai na kare hakkokin ta.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

Yayin tattaunawar manyan jami’an, bangaren Sin ya fayyace matsayarsa ga Philippine, wadda ta kuskurewa gaskiyar lamarin, ta yi gaban kan ta, har ma ta yi hadin kai da wasu sassa na waje, wadanda ba sa ga maciji da juna da Sin. Philippine ta ci gaba da aiwatar da matakan tada husuma, sai dai a na ta bangare, Sin za ta yi duk mai yiwuwa, wajen kare hakkokin ta kamar yadda doka ta tanada, tare da maida martani idan akwai bukatar hakan. Wannan wani gargadi ne a fayyace, wanda muke fatan zai sanya Philippines fahimta, da lura da halin da ake ciki, kana ta tsaya kan gaskiya a kalamanta da matakan da take aiwatarwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana

Next Post

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

Related

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

5 hours ago
Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi
Daga Birnin Sin

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

6 hours ago
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

7 hours ago
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

7 hours ago
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

8 hours ago
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

10 hours ago
Next Post
Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

May 23, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

May 23, 2025
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

May 23, 2025
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

May 23, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

May 23, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

May 23, 2025
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.