ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

by Leadership Hausa
2 years ago
Hakar

A kwanan nan Ministan Ma’adanai, Mista Dele Alake, ya bayyana alakar hakar ma’adanai da bisa ka’ida ba da ayyukan ta’addanci a kasar nan. A ta bakinsa, “Yawancin ayyukan ta’addanci da na ‘yan bindiga masu harkokin hakar ma’adanai ba bisa ka’idaba suke daukar nauyinsu a Nijeriya. Ba wai wadanda suke aikin hakar ainihin ma’adanan ba ne amma manyan masu kudi ne a sassan Nijeriya suke daukar nauyin ta’addancin”. A ra’ayinmu da muka wallafa a wani lokaci a baya mun yi irin wannan bayanin.

Mun sake dawo da sharhin ne don ya zama kalubale ga gwamnati domin ta samo hanyar warware matsalar. Dole ne a fallasa tare da kunyata wadannan mutanen. Minista Alake zai iya jagorantar wannan fafatawar.

  • Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana
  • Gwamnan Zamfara Ya Gabatar Da Kasafin N432.5b Shekarar 2024

Al’amarin da ya shafi dangantakar ayyukan ta’addanci da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Nijeriya ya kara fitowa fili ne a wani rahoto da wata jaridar kasar Birtaniya ta ruwaito kan yadda ‘yan kasuwar kasar Sin suka mamaye harkar hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba kuma suke tallafa wa masu ayyukan ta’addanci a sassan Nijeriya. Jaridar ta kuma kara da cewa, ‘yan kasar Chanan suna cimma wannan buri nasu ne ta hanyar bayar da cin hanci ga wasu bangarori da al’ummar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Amma kuma nan take ofishin jakadancin kasar Chana a Nijeriya ya karyata wannan zargin, tare da bayyana cewa babu cikakkun hujjoji na danganta kasar Chana da ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Yana da matukar muhimmaci a fahimci cewa, ba wannan ne karo na farko ba da ‘yan Nijeriya ke lura da cewa, ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba yana taimaka wa ayyukan ‘yan ta’adda a sassan Nijeriya. Wannan yana kara fitowa fili ne in aka lura da yadda ‘yan bindigar ke fuskantar jami’an tsaronmu da makamai na zamani masu karfi da kuma yadda suke yada farfaganda don dakile gaskiyar halin da ake ciki. A lokuta da dama wadannan ‘yan ta’addar suna tafka ayyukan ta’addanci ba tare da an hukunta su ba.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

A matsayinmu na gidan jarida, mun yi imanin cewa, ba zai yiwu a ce, wadannan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba suna aikata ayyukan ta’addanci ba tare da an hukunta su ba, ya kamata hukumar da ke bayar da izinin hakar ma’adanai ta soke lasisin wadannan kamfanonin da ake zargi in ba haka ba to lallai dole ministan ma’adanai ya fito fili ya yi bayani mai gamsarwa a kan lamarin.

Tun da farko mun kafa ayar tambaya a kan yadda hamshakan masu kudi ke tafiyar da harkar hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, amma kuma idan har akwai hannun wasu kasashen waje a ayuyykan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba to mun san hakan ba zai taba yiwuwa ba sai an samu hadin kan ‘yan Nijeriya.

Yana da matukar muhimmnanci a fahimmci cewa, Nijeriya na da mutane da kowacce al’umma ke mutuntawa suna kuma daukar su da matukar muhimmanci, irin wadannan mutane ne suke daukar nauyin shigowar ‘yan kasashen waje ta hanyar samar musu da Biza da sauran ka’idojin da suke bukatar cikawa, in ma sun samu matsala su ne dai ke tabbatar da ba a hukunta su ba a lokuta da dama. Wannan ne yake kara bayyana mana ainihin dalilin da ya sa suka samu hanyar shigowa cikin kasa tun da farko.

Harkar hakar ma’adanai ba wata abu ba ne da za a iya yi a boye, abu ce da ke bukatar manyan kayan aiki da ma’aikata na cikin gida da kasashen waje yana kuma bukatar zuba jari mai yawan gaske. Ana kuma fitar da abin da aka samu ta hanyoyin shiga da fita kasar nan (ta kasa, ruwa da ta sama). Akwai kuma jami’ai da hukumomin da aka dora wa alhakin kula da wadanna kafofi, shin suna sane da ayyuykan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ko kuma suna yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ne?

In har ta hanyar ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba Nijeriya na asarar kudaden shiga to mene ne jami’an tsaronmu da sauran hukumomin gwamnati ke yi don dakile ayyukan masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa?

A ra’ayinmmu, babu wani aiki na masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a halin yanzu sai da kawai tare da ayyukan wasu tsageru da suke amfani da tabarbarewar harkoki a kasa na abin da ya shafi cin hanci da rashin iya gudanar da aiki a ma’aikatun gwamnnati don cutar da tattalin arzikin kasa, suna daukar nauyin ‘yan ta’adda don su dauke hankali daga ainihin abin da ke faruwa a yankunan kasar nan inda wasu ‘yan kalilan ke tatsar dukiyoyin kasa.

A duk lokacin da aka samu hannun kasashen waje a harkokin hakar ma’adanai dole a fuskanci matsalolin tsaro, muna da darussa daga abin da ya faru a kasashe irin su Saliyo da Kongo. Duk da cewa, majalisar dinkin duniya na da hanyoyin da take fuskantar irin wadannan matsalolin. Ya kamata kafin tarayyar kasashen duniya su kawo mana dauki dole gwamnatin Nijeriya ta amince da cewa, lallai akwai matsala a bangaren hakar ma’adanai a kasar nan, ta kuma dauki matakin da suka dace don magance yadda masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ke cin karensu babu babbaka, dole gwamnati ta toshe duk wata kafa kafin a kai ga dora wani laifi a kan wani. Ya kamata gwamnati ta dauki kudurin fuskantar lamarin kai tsaye ba tare da nuna tsoro ba.

Hakar
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja

Rayuwar 'Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.