• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bazan Daukaka Kara Ba, Na Amince Da Hukuncin Kotu Akan Mazabar Yobe Ta Arewa —Lawan

by Muhammad Maitela
3 years ago
Lawan

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Lawan ya ce ba zai daukaka kara ba kan hukuncin da babbar kotun tarayya da ke Damaturu a jihar Yobe ta yanke ranar Laraba kan zaben Sanatan Yobe ta Arewa da ke gabatowa ba.

Sanata Lawan ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwar manema labaru wadda ya sanya wa hannu kuma ya fitar a ranar Alhamis, inda ya ce ya amince da hukuncin da kotu ta yanke na hana shi takara da kuma shiga zaben.

  • 2023: Rashin Halartar Osibanjo, Lawan, Amaechi Ya Janyo Dakatar Da Zaman Sulhun APC

A cikin sanarwar ya kara da cewa, “A jiya Laraba 28 ga watan Satumba, 2022, babbar kotun tarayya dake Damaturu ta yanke hukunci kan wanda ya cancanta ya tsaya takarar Sanatan Yobe ta Arewa a zaben 2023. Wanda hukuncin da aka ce ya hana ni tsayawa takara don haka na shiga zaben.”

“Wanda bayan tuntubar juna da abokanan siyasa da magoya bayana da sauran wadanda suka dace na tuntuba, na yanke shawarar ba zan daukaka kara kan hukuncin ba, na amince da hukuncin.”

“A halin da ake ciki, ina ganin ya dace in gode wa mai girma Sanata Ibrahim Gaidam bisa rawar da ya taka a siyasar jam’iyyar APC a jihar Yobe, ina kuma gode wa mai girma Gwamna Mai Mala Buni bisa goyon bayan da ya bani tare da nuna yanuwantaka.”

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

“Ga kuma al’ummar mazabana, ina gode muku baki daya bisa goyon bayan da kuka bayar, da biyayya da sadaukarwar da kuka yi na gina al’ummarmu da yankin Yobe ta Arewa da ma jihar Yobe baki daya.”

“Ina so in kara tabbatar muku cewa zan ci gaba da yi muku hidima a cikin kaina da kuma kowane irin aiki a kowane lokaci.”

“Mun yi tafiya tare tsawon lokaci, kuma wannan tafiya za ta ci gaba da zama doguwar tafiya mai tsawo, dangantaka ce mai ban sha’awa kuma ba za ta iya yin karfi ba. Ina bin ku duka, Alhamdulillah.” In ji Sanata Lawan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Next Post
Gwamna Bello Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sarkin Lokoja

Gwamna Bello Ya Yi Ta'aziyyar Rasuwar Sarkin Lokoja

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.