• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 hours ago
CIIE

Mataimakin kwamishinan kula da harkokin zuba jari da kasuwanci na shiyya-shiyya, dake karamin ofishin jakadancin Najeriya da ke birnin Shanghai Hassan Mohammed, ya rataye takardun izinin shiga taruka da dama da ya taba halarta a ofishinsa. Daga cikinsu, takardun shiga bikin baje kolin hajojin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE suna kan gaba.

Mohammed ya halarci dukkan bikin baje kolin CIIE guda 7 da aka gudanar a baya, kuma ya ganewa idonsa yadda ‘yan kasuwa masu sayar da dangin gyadar shazawa ko “cashew” daga Najeriya suka shigo kasuwar Sin ta hanyar baje kolin na CIIE.

A lokacin baje kolin da ya gabata, an ba da damar baje kolin dangin gyadar ta “cashew” daga Najeriya, matakin da ya haifar da karin kasuwanci tsakanin Sin da Najeriya a wannan bangare, ya kuma baiwa ‘yan kasuwa daga Najeriya damar shiga kasuwar Sin. Mohammed ya yi imanin cewa, baje kolin na CIIE ya bude hanya ga ‘yan kasuwar Najeriya ta samun nasarar kasuwanci. Ya ce “‘Yan kasuwa daga Najeriya sun kafa kamfanoni tare da ‘yan kasuwar kasar Sin, wanda hakan ya ba su damar fadada samar da kayayyaki, da habaka ayyukan yi a Najeriya, da kuma samun karin kudin shiga ga jama’a.”

Baya ga kasuwar Sin, Najeriya ta samu damar kulla hada-hadar kasuwanci da sauran sassa na duniya ta hanyar baje kolin na CIIE. Wani dan kasuwar Georgia, ya kulla yarjejeniyar ciniki da dan kasuwar Najeriya game da ridi a yayin taron na CIIE. Game da hakan, Mohammed ya bayyana cewa, kasancewar nisan da ke tsakanin kasashen biyu, idan ba don damar da CIIE ta samar ba, da wannan ciniki ya kasance mai wahala.

Yayin da ake daf da bude bikin baje koli na CIIE karo na 8, ana sa ran karin kayayyakin amfanin gona masu inganci daga Nijeriya za su shiga kasuwar Sin ta wannan dandali. Sin za ta ci gaba da bude kasuwanninta bisa nagartattun manufofinta ga duniya ta hanyar CIIE, tare da taka rawar gani wajen inganta hadin gwiwa da cin moriyar juna tsakanin kasa da kasa. (Mai Zane da Rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Next Post
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.