• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bikin Baje-Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Zai Kara Inganta Hadin-Gwiwar Bangarorin Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Alhamis 29 ga wata ne, aka kaddamar da bikin baje-kolin tattalin arziki da cinikayya na kasashen Sin da Afirka karo na uku a birnin Changsha na lardin Hunan na kasar Sin, wato China-Africa Economic and Trade EXPO. Ana sa ran cewa, bikin na bana zai kara taka muhimmiyar rawa, da baje karin hajojin Sin da Afirka, al’amarin da zai sanya sabon kuzari ga hadin-gwiwar bangarorin biyu.

Yawan kamfanonin cikin gida da waje da suke halartar bikin na bana, ya kai 1500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari idan aka kwatanta da bikin da ya gabata. Kana, kayayyaki 1590 daga kasashe 29 ne, aka yi rajistar shigar da su baje-koli na bana. Ana kuma shirin rattaba hannu ko kuma gudanar da shawarwari kan wasu ayyukan hadin-gwiwa guda 218, wadanda jimillar darajarsu ta kai dala biliyan 19.1.

  • Sin Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwarta Da Afrika

A bana ne ake cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kasar Sin ta yi, kana shekaru 10 da kasar ta fitar da muhimman manufofinta kan nahiyar Afirka, wato nuna “Sahihanci”, da “Sakamako na hakika”, da “Dangantakar abokantaka”, da kuma “Aminci”. A cikin wadannan shekaru 10, kwalliya ta biya kudin sabulu, wajen karfafa hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da kasuwanci.

Bikin baje-kolin tattalin arziki da cinikayyar Sin da Afirka, dandalin hadin-gwiwa ne mafi girma a karkashin tsarin FOCAC, wato dandalin tattauna hadin-kan Sin da Afirka. Tun daga shekara ta 2019, a kan shirya irin wannan biki bayan kowane shekaru biyu-biyu. A ranar 2 ga watan Yuli ne, za a kammala bikin na bana.

Sannan, a yau Alhamis, babbar hukumar kwastan ta kasar Sin ta gabatar da alkaluman cinikayya tsakanin Sin da Afrika karon farko yayin bikin baje kolin harkokin cinikayya na Sin da Afrika karo na 3. Bisa alkaluman, makin cinikayya a shekarar 2000 ya kai 100, yayin da a shekarar 2022 ya karu zuwa maki 990.55, abin da ya bayyana saurin bunkasuwar cinikayyar bangarorin biyu. A cikin wadannan shekaru kuma, yawan kudin dake shafar cinikin kayayyakin da Sin ke fitarwa zuwa Afrika ya ninka fiye da sau 20, wanda ya karu da kashi 17.7 a ko wace shekara. Hakan ya sa Sin ta kai matsayin koli a fannin ciniki da Afrika a cikin shekaru 14 a jere.

Labarai Masu Nasaba

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

A wannan rana kuma, an bude dandalin hadin kai a fannin kiwo lafiyar bil Adama da tsirrai tsakanin Sin da Afrika wato SPS a birnin Changsha, hedkwatar lardin Hunan. Yayin dandalin, wakilin babbar hukumar kwastan ya yi bayani kan nagartattun matakai da za su tabbatar da kafa hanyar samar da rangwame ga kayayyakin aikin gona da Sin za ta shigo da su daga Afrika. (Murtala Zhang, Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Musanta Hana Tinubu Binciken Tsofaffin Jami’an Gwamnatinsa 

Next Post

Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

Related

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka
Daga Birnin Sin

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

5 hours ago
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

6 hours ago
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

6 hours ago
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe
Daga Birnin Sin

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

8 hours ago
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

8 hours ago
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya
Daga Birnin Sin

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

9 hours ago
Next Post
Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

Mahalarta Taron Davos Sun Ba Da Labarin Ci Gaban Sin

LABARAI MASU NASABA

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Gwamna Yusuf

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

September 2, 2025
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

September 2, 2025
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.