ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Bazara: Gagarumin Bikin Da Duniya Ke Jira

by CGTN Hausa
2 years ago
Bikin bazara

A yayin da al’ummar Sinawa ke shirye-shiryen bikin bazara wato Spring Festival a Turance, bikin gargajiya mafi kasaita ga Sinawa, dake alamanta shiga sabuwar shekara bisa kalandar gargajiya ta kasar, haka ma al’ummar duniya ke jiran wannan kasaitaccen biki mai tsawon tarihin da ya kai kimanin shekaru 4000, wanda ya fado a ranar 10 ga watan Fabrairun shekarar 2024. Rahotanni na nuna cewa, yawan zirga-zirgar fasinjojin da suka yi tafiye-tafiye ta jiragen kasa a kasar Sin a ranar 5 ga wata kadai, ya kai miliyan 12 da dubu 198. Kana a ranar 6 ga wata, ana hasashen adadin zai karu, inda ake zaton zai kai miliyan 12 da dubu 900, wannan ya sa aka kara samar da jiragen kasa 1789. A halin yanzu, zirga-zirga ta jiragen kasa a dukkan kasar Sin na gudana yadda ya kamata, kuma harkokin zirga-zirgar jiragen kasa na komawa kamar yadda aka saba a tashoshin jiragen kasa da matsalar yanayi ta shafa.

Lokacin bulaguro na bikin bazara na kasar Sin na bana yana daukar kwanaki 40 daga ranar 26 ga watan Janairu zuwa 5 ga watan Maris. Hukumomin zirga-zirga da sufuri na kasar Sin sun yi hasashen cewa, mutane kimanin biliyan 9 ne za su yi zirga-zirga tsakanin yankuna a fadin kasar a cikin wannan lokaci, wanda ya kusan ninka adadin a shekarar 2023. Wannan a cewar masu fashin baki, ya kara nuna yadda al’ummar Sinawa ke daukar al’adunsu na gargajiya da matukar muhimmanci, duk da ci gaban zamani, hakan bai sanya su watsi da al’adunsu ba.

  • Kasar Sin Ta Taya Nangolo Mbumba Murnar Zama Sabon Shugaban Namibia
  • Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

Babbar manufar wannan biki mai muhimmanci ga Sinawa, ba ta sauya ba a tsawon shekaru masu yawa, wato haduwa da iyalai bayan tsawon shekara, don murnar shigowar sabuwar shekara bisa kalandar gargajiyar kasar Sin.

ADVERTISEMENT

A kowace shekara, Sinawa na amfani da dabbobi 12 domin wakiltar kowace shekara, a bana sabuwar shekarar gargajiya ta Sin shekara ce ta dabbar Loong. Sauran dabbobin dake alamta kowace shekara sun hada da Bera, da Saniya, da Damisa, da Zomo, da Maciji, da Doki, da Rago, da Biri, da Kaji da Kare da kuma Alade.

Saboda tasiri da muhimmancin wannan biki, yanzu haka an nuna dandanon shagulgulan bikin na bana a kasashe da dama na duniya, da suka hada da Brazil da Rasha, da Najeriya da Masar, da Amurka da Habasha da Kenya da sauransu. Kuma idan ba a manta ba a karshen shekarar da ta gabata ce, babban taron MDD karo na 78 ya zartas da kudurin sanya bikin bazara, a matsayin lokacin hutu na MDD, baya ga kusan kasashe 20 na duniya da suka ayyana bikin bazara a matsayin lokacin hutu a hukumance, yayin da kusan kashi daya bisa biyar na al’ummar duniya ke murnar bikin bazara ta hanyoyi daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Babban sako ga daukacin al’ummar duniya shi ne, kowa ya rike al’adarsa da muhimmancin gaske, domin kayan aro ba ya rufe katara. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
Daga Birnin Sin

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Kwamitin Asusun Samar Da Tallafin Tsaro

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Kwamitin Asusun Samar Da Tallafin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.